• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Likitoci Sun Ja Daga A Kan Dokar Yin Aiki Na Shekara Biyar

by Sabo Ahmad
2 years ago
in Labarai
0
Likitoci Sun Ja Daga A Kan Dokar Yin Aiki Na Shekara Biyar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yanzu haka dai majalisar wakilai na kokarin kafa dokar da za ta hana likitoci kasar waje har sai sun yi shekara biyar bayan sun kammala karatunsu.

Wannan matakin da majalisar ke kokarin dauka ya biyo baya ganin yadda likitocin ke turuwar zuwa kasashen waje domin yin aiki a can.

  • Ministocin Wajen Kasashen Sin Da Rasha Da Pakistan Da Iran Sun Tattauna Game Da Batun Afghanistan
  • Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Bunkasa Da Kaso 4.8% A Rubu’in Farko Na Bana Duk Da Raguwar Bukatun Waje

Ficewar likitocin wani babban kalubale ne ga al’ummar Nijeriya wanda hakan ya sa kasar fuskantar karancin ma’aikatan lafiya.

Wanna hali da aka fada na ficewar likitocin babban koma-baya ne a shanin kiwon lafiyar al’ummar kasar nan.

Kamar yadda Hukumar kula da lafiya ta duniya ta bayyana Njeriya na fuskantar barazanar babba ta ficewar likitocinta.

Majiyarmu ta tabbatar mana da likitocin ke fita zuwa kasashen tarayyar Turai.

Jami’an lafiya sun tabbatar da cewa, a kalla likitoci 5,600 daga kasar nan suka tafi tarayya Turai a cikin shekara takwas da suka wuce.

A shekara ta 2022, kungiyar likitoci ta Nijeriya ta ce za a samu kima-baya a fannin lafiya matukar gwamnati ba ta dauki matakan da suka kamata ba wajen kawo karshen ficewar likitocin ba. Saboda haka kungiyar ta bukaci gwamnati ta gaggauta kawo karshen ficewar likitocin.

Haka kuma a farkon wannan shekarar shugaban kungiyar likitocin na kasa kuma shugaban kungiyar likitocin hakora Dakta Bictor Makanjuola ya bayyana cewam fiye da likitoci 500 suka bar kasar nan cikin shekara biyu da suka wuce .

Saboda haka kungiyar likitoci ta kasa reshen jihar Kaduna ta bukaci a dauki matakin gaggawa domin kawo karshena kwararewar liktocin daga jihar Kaduna. Kungiyar ta nuna cewa,kusan likitoci 10,000 suka tafi wasu kasashe.

Su ma kungiyar gwamnonin kasar nan sun nuna damuwarsu kan yadda likitocin ke fita.

Shugaban kungiyar Aminu Waziri Tambuwal,ya nuna damuwarsa kan ficewar likitocin, da kuma yadda za samo bakin zaren, lokacin da ya ziyarci ministan lafiya Dakta Osagie Ehanire, a Abuja.

Zaben Shugabanin Majalisa: An Nemi APC Ta Daidaita Tsakanin Kudu-maso-kudu Da Arewa-maso-yamma

Akwai yiwuwar jam’iyyar APC ta raba mukamin shugaban majalisa da mataimakinsa tsakanin Kudu-maso-kudu da shiyyar Arewa-maso-yamma.

Koda yake har yanzu jam’iyyar ba ta fitar da wata matsaya ba kan shugabancin majalisat ta 10 ba, sai wasu kafofi daga fadar shugaban kasa, sun nuna cewa, shiyyar Kudu-maso-kudu na iya samun shugaban majalisar.

Jam’iyyar APC ta samu nasara kujeru 57, yayin da ita kuma PDP, ke da guda 27.

 Sauran su ne LP da ta samu 6; NNPP ta samu 2; da SDP, 2, sai YPP da APGA wadda kowanneneu ta samu 1.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Zuwa yanzu wadanda ke sa ran za su iya samun samun shugabanci majalisar ta 10 sun hada da shugaban majalisar na yanzu Ahmad Lawan na jam’iyyar APC, daga Yobe ta Kudu sai Sanata Sani Musa  na APC daga Neja-ta-gabas sai Sanata Chief Whip sai Sanata Orji Uzor Kalu na APC daga Abiya ta arewa sai Sanata Jibrin Barau na APC daga Kano ta Arewa sai Sanata Godswill Akpabio na APC, Akwa Ibom ta Arewa-mas-yamma.

Sai kuma Mataimakin shugaban majalisar dattawa, Sanata Abdul Ningi  na APC daga Bauchi ta tsakiya da kuma Sanata Abdul- Aziz Yari na APC daga Zamfara).

Haka kuma gwamna Dabid Umahi na APC da Ebonyi South da Adams Oshiomhole na APC daga Edo ta Arewa dukkaninsu sun nuna sha’awar zama shugaban majalisar.

Haka kuma Sanata Ali Ndume daga Borno da Sanata Osita Izunaso daga jihar Imo su ma sun nuna sha’awarsu.

Sai dai har zuwa wannan lokaci jam’iyyar na ci gaba da tuntuba kan shugabancin majalisar yadda za ta tabbatar da wanda zai bayar da cikakkiyar gudummowa wajen bunkasa kasa da hada da zababben shugaban kasa Bola Tinubu don samun ci gaba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AikiLikitoci
ShareTweetSendShare
Previous Post

GORON JUMA’A

Next Post

Ya Sheka Barzahu Bayan Dirkar Kwayar Tiramadol

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

6 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

7 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

8 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

13 hours ago
Likitoci
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

13 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

14 hours ago
Next Post
Ya Sheka Barzahu Bayan Dirkar Kwayar Tiramadol

Ya Sheka Barzahu Bayan Dirkar Kwayar Tiramadol

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.