• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Yi Gangamin Nuna Goyon Bayan Falastinu A Bauchi

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
An Yi Gangamin Nuna Goyon Bayan Falastinu A Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A Juma’ar nan ne dubban jama’a suka fito kan titi inda suka zagaye gari da nufin nuna goyon bayansu ga al’umman Palastinu wanda Yahudawa ke zalumta kamar yanda masu gangamin suka bayyana.

 

Malam Ahmad Yusuf Yashi, wakilin ‘yan uwa musulmai almajiran Sheikh Ibrahim Zakzaky na jihar Bauchi ne ya jagoranci masu zagayen garin, ya bayyana cewar sun fito ne domin amsa kiran Ayyatullahi Imam Khumaini na kiran illahirin jama’a da suke amfani da ranar Juma’ar karshen ramadana wajen tunawa da raunanan Palasdinawa da kuma sauran wadanda ake zalumta a fadin duniya.

  • Likitoci Sun Ja Daga A Kan Dokar Yin Aiki Na Shekara Biyar

“Shi wannan massalacin na Quds shi ne masallaci na uku a daraja amma an wayi gari yana karqashin ikon Yahudawan Sahayoniya kuma wajibi ne mu kwato wannan massalacin domin na musulmai ne,” a cewarsa

 

Labarai Masu Nasaba

An Kammala Baje Kolin Hada-Hadar Cinikayyar Hidimomi Na Sin Na Shekarar 2025

Me Ya Sa Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Ta Samu Goyon Baya Daga Sassan Kasa Da Kasa

Ya kuma qara da cewa a irin wannan ranar su na kuma tuna da kuma yin dubiya kan halin da sauran jama’an duniya ke ciki musamman wadanda ake zalumta.

 

A cewar Ahmad Yashi sun fito ne domin su goyi bayan al’ummar Falastinu tare da tir da zalumcin da Yahudawa ke yi wa al’ummar Falastinuwa, ya nuna cewa shirin Yahudawa ba ga zallar Falastinuwa ya tsaya ba so suke su mamaye yankin Gabas ta tsakiya baki daya.

 

Ya ce: “Wannan fitowa da muke yi ba ma ga zallar Falastinuwa ba ne, a gaskiyar magana don dukkanin musulman duniya da raunanan da suke rayuwa a doron kasa. Domin da Isra’ila za ta yi nasara kawar da wadanda suke Palastinu to za ta mamaye dukkanin Gabas ta Tsakiya ne, wadannan kasashen irinsu Lebonon, Siriya, Jordan, Yusra da makamantansu. Domin ta taba gwada wannan yunkurin nata a 1967 na mamaye sassan wadannan wuraren.

 

“Su na nan suna da wannan tunanin da wannan burin. A takaice ma har sun bai wa shirinsu suna da cewa za su samar da Isra’ila babba wanda sun ce za su hada har da Madina daman sun ce Madina kasarsu ce, Annabi da ya zo ne ya koresu a nan.

 

“Don haka ya kamata musulmai su shiga cikin hayyacinsu ba magana ce ta ‘yan Shi’a ko ‘yan kaza ba. A’a lamari ne da ya shafi musulman duniya baki daya da duk kuma wanda yake da rauni a doron kasa. Kiranmu a nan shi ne al’umma ta zo da Sunnanta da Shi’anta a fito a yi Allah wadai da abun da Yahudawa ke yi a wannan yankin da kuma nuna goyon baya ga al’ummar Falastinu. Kuma insha Allahu nasara na nan tafe ga al’ummar Falastinu,” ya tabbatar.

 

Wakilinmu da ya kasance da muzaharar ya shaida mana cewar masu muzaharar sun yi ta waken bayyana halin da al’ummar Falasdinawa ke ciki, da kuma nuna goyon bayansu a garesu. An yi zagayen lafiya aka kuma tashi a cikin garin na Bauchi


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Na Tsayawa Tsayin Daka Kan Matsayinta Game Da Batun Basussukan Kasashe Masu Tasowa

Next Post

Yadda Za Ki Tsara Kwalliyarki Ranar Sallah

Related

An Kammala Baje Kolin Hada-Hadar Cinikayyar Hidimomi Na Sin Na Shekarar 2025
Daga Birnin Sin

An Kammala Baje Kolin Hada-Hadar Cinikayyar Hidimomi Na Sin Na Shekarar 2025

39 minutes ago
Me Ya Sa Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Ta Samu Goyon Baya Daga Sassan Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

Me Ya Sa Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Ta Samu Goyon Baya Daga Sassan Kasa Da Kasa

2 hours ago
An Karrama Fitattun Fina-Finai A Bikin “Golden Panda” Da Ya Gudana A Lardin Sichuan Na Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Karrama Fitattun Fina-Finai A Bikin “Golden Panda” Da Ya Gudana A Lardin Sichuan Na Kasar Sin

3 hours ago
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Daga Birnin Sin

An Kama Wani Sojan Gona Ɗauke Da Bindiga A Katsina

4 hours ago
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya
Daga Birnin Sin

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

23 hours ago
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

1 day ago
Next Post
Yadda Za Ki Tsara Kwalliyarki Ranar Sallah

Yadda Za Ki Tsara Kwalliyarki Ranar Sallah

LABARAI MASU NASABA

Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan

Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan

September 14, 2025
An Kammala Baje Kolin Hada-Hadar Cinikayyar Hidimomi Na Sin Na Shekarar 2025

An Kammala Baje Kolin Hada-Hadar Cinikayyar Hidimomi Na Sin Na Shekarar 2025

September 14, 2025
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi

September 14, 2025
Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

September 14, 2025
Me Ya Sa Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Ta Samu Goyon Baya Daga Sassan Kasa Da Kasa

Me Ya Sa Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Ta Samu Goyon Baya Daga Sassan Kasa Da Kasa

September 14, 2025
Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa

Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa

September 14, 2025
Me Ya Sa Bayern Liverkusen Ta Kori Erik Ten Hag Bayan Wasanni Biyu?

Me Ya Sa Bayern Liverkusen Ta Kori Erik Ten Hag Bayan Wasanni Biyu?

September 14, 2025
An Karrama Fitattun Fina-Finai A Bikin “Golden Panda” Da Ya Gudana A Lardin Sichuan Na Kasar Sin

An Karrama Fitattun Fina-Finai A Bikin “Golden Panda” Da Ya Gudana A Lardin Sichuan Na Kasar Sin

September 14, 2025
Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

September 14, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Wani Sojan Gona Ɗauke Da Bindiga A Katsina

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.