ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Bayern Liverkusen Ta Kori Erik Ten Hag Bayan Wasanni Biyu?

by Abba Ibrahim Wada
9 months ago
Kori

Kwanaki kaɗan bayan kama aiki a ƙungiyar Bayer Leɓerkusen, tsohon mai horas da Manchester United Eric Ten Hag ya gaza jagorantar ƙungiyar na tsawon ko da mako 10.

Ba mako 10 ba ma, ko mako 9 bai cika ba, inda ya yi kwana 62 kacal a ƙungiyar, bayan buga wasan gasar Bundesliga biyu kacal. An kore shi ne bayan Leɓerkusen ta gaza yin nasara a karawarta da Werder Bremen a ranar Asabar. Da farko Leɓerkusen ce ta shige gaba da ci 3-1, inda Bremen ta samu jan kati, amma daga baya aka tashi wasan canjaras 3-3.

  • Al Hilal Za Ta Biya Yuro Miliyan 53 Don Ɗaukar Nunez Daga Liverpool
  • Barcelona Ta Tube Ter Stergen Daga Mukaminsa Na Kaftin Din Kungiyar 

Hakan ya biyo bayan kashin da Leɓerkusen ta sha a gida a hannun Hoffenheim a wasanta na farko na gasar Bundesliga na wannan kaka. Wasa ɗaya ne kacal Ten Hag ya samu nasara a matsayin mai horas da Leɓerkusen.

ADVERTISEMENT

An naɗa Ten Hag a muƙamin ne a ƙarshen watan Mayu domin maye gurbin tsohon kocin ƙungiyar Ɗabi Alonso, wanda ya koma Real Madrid. Da farko, Leɓerkusen ta yi tsammanin zai iya jan ragamar sake gina ƙungiyar bayan rasa ƴan  wasanta irin su Florian Wirtz da Jonathan Tah.

To sai dai sakamakon wasannin farko-farko na wannan kakar ba su yi kyau ba, amma ba wannan ne babban dalili ko kuma ɗaya daga cikin manyan dalilan da suka haifar da korar Ten Hag ba. Kusan tun farko Ten Hag ya fara shafa wa kansa baƙin fenti sanadiyyar wasu matakai da ya ɗauka da kuma halayyarsa.

LABARAI MASU NASABA

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

Misali, ya sauya lokacin da aka tsara yin wasan sada zumunta da ƴan  ƙasa da shekara 20 na ƙungiyar Flamengo a lokacin da Leɓerkusen ta je atisaye a Brazil. An buga wasan kwana biyar kafin ranar da aka tsara tun farko, inda Leɓerkusen ta sha kashi da ci 5-1.

Haka nan a kusan wannan lokacin ne Ten Hag ya yanke hukunci kan batun tafiyar Granit Ɗhaka, inda ya ce ya kamata ya tsaye saboda Leɓerkusen ta rasa manyan ƴan  wasa da yawa.

Sai dai tuni ƙungiyar ta sanar cewa Ɗhaka zai iya tafiya idan aka samu tayi mai kyau. Daga baya ya tafi Sunderland. Haka nan kuma Ten Hag ya soki ƴan  wasansa tare da cewa ba su da kuzarin da ya kamata duk da cewa shi da tawagarsa ne suka jagoranci tawagar.

Bugu da ƙari an zargi Ten Hag da rashin kwarjinin da ake koci ke buƙata domin jan ragamar babbar ƙungiya, musamman ma ƙungiyar da ta kawo sabbin ƴan  wasa da dama.

Za a iya cewa da alama ya riƙa shan wahala wajen shawo kan ƴan  wasa su bi tsarinsa, domin wasu majiyoyi sun ce bai iya yi wa ƴan  wasa wata ƙwaƙƙwarar huɗuba gabanin buga wasa. Sannan an bayyana cewa bai yi wa ƴan  wasan jawabi ba gabanin karawarsu ta farko da Hoffenheim. Akasin Alonso, wanda aka ce shi ya riƙa ƙarin ganin ya ƙara ƙwarewa a harshen Jamusanci tare da samun ƙarin gogewa lokacin da yake jagorantar ƙungiyar ta Leɓerkusen.

Abin ya ba da mamaki sosai yadda shugabannin Leɓerkusen suka yanke shawarar korar Ten Hag da wurwuri haka domin wannan ba abu ne mai alfanu ba ga daraktan wasanni na ƙungiyar Simon Rolfes – wanda ya dage kan a ɗauki Ten Hag a lokacin da ƙungiyar ke son ɗaukar sabon koci a watan Mayu – har ma da shugaban ƙungiyar Fernando Carro.

A ƴan  shekarun da suka gabata Ten Hag ya kasance ƙwararren mai horaswa lokacin da ya samu nasara sosai a Ajaɗ. Ya lashe gasar Holland sau uku sannan ya kai wasan kusa da na ƙarshe a gasar zakarun nahiyar Turai ta Champions League a shekara ta 2019.

Ko a shekarar farko na jagorancin Manchester United aikinsa ya yi kyau babu laifi, kuma an alaƙanta barin aikinsa daga ƙungiyar kan rikicin da ƙungiyar ta fuskanta amma ba domin gazawarsa a matsayin mai horaswa ba. Amma a yanzu Leɓerkusen da alama tana cikin ruɗani. Kusan za a iya cewa a shirye suke su sayer da duk wani ɗan wasa da ya nuna aniyar barin ƙungiyar. A lokaci guda kuma ƴan  wasa irin su Malik Tillman da Jarell Ƙuansah sun tafi ƙungiyar tare da sa ran cewa Ten Hag ne zai ci gaba da horaswa.

A yanzu Leɓerkusen na buƙatar nemo wanda zai maye gurbinsa. Akwai rahotannin cewa sun tattauna da tsohon kocin Barcelona Ɗaɓi, haka nan kuma tsohon mai horas da Dortmund da Leipzig Marco Rose na cikin waɗanda ake ganin za su iya samun aikin.

Kori
Abba Ibrahim Wada
+ postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Har Yanzu Nijeriya Tana Fatan Zuwa Kofin Duniya Na 2026
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Mece Ce Matsalar Real Madrid? 
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Ko Ka San Dalilin Da Zai Bai Wa Nijeriya Damar Zuwa Gasar Cin Kofin Duniya?

MASU ALAKA

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya
Wasanni

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa
Wasanni

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

June 2, 2026
Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta
Adabi

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

May 31, 2026
Next Post
Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa

Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.