• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Inuwa Ya Bukaci Musulmai Su Ci Gaba Da Habbaka Darussan Ramadana

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Inuwa

Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ya buƙaci al’ummar jihar su ci gaba da gudanar da ayyukan su na ibadah da suka yi a watan na Ramadana, da addu’o’in zaman lafiya da ci gaban jihar da Nijeriya baki daya. 

 

Gwamnan ya yi wannan kiran ne a sakon sa na Barka da Sallah da Ismaila Uba Misilli, hadiminsa a bangaren yada labarai da hulda da jama’a ya fitar.

  • Inuwa Ya Bai Wa ‘Yan Kasuwan Gombe Kyautar Naira Miliyan 500 Don Karfafa Kasuwancinsu 

Gwamna Inuwa, wadda ya bayyana sallar Eid-el-Fitr a matsayin lokacin tunani da nazari kan rahamomin Allah ga bayi, ya bukaci al’ummar Musulmi su rinka dabbaƙa darusan da suka koya a watan na Ramadan a rayuwar su ta yau da kullum.

 

LABARAI MASU NASABA

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

Ya ce, “Yayin da muke bukukuwan Eid-el-Fitr, ina yi mana nasiha da mu yi koyi da kyawawan darussa na watan Ramadan wadanda suke nuni da takawa, da biyayya, da sadaukarwa. Dole ne dukkan mu mu yi koyi da koyarwar Musulunci da ke tabbatar da zaman lafiya da hakuri, da kana’a da kuma kauna”.

 

Gwamna Inuwa ya kuma bukaci al’ummar jihar da cewa kar su sare game da kalubalen zamantakewa da na tattalin arziƙin da ake fuskanta a kasar nan, amma su jajirce wajen yin addu’o’i, yana mai cewa idan suka jajirce, jarabawar da ake ciki za ta wuce, kuma Nijeriya za ta kara karfi da karsashi da hadin kai.

 

Ya kuma bukaci jama’a su ci gaba da ririta zaman lafiya da kwanciyar hankali da ake da shi a jihar, inda ya yi kira ga malamai da sarakuna su ci gaba da wa’azin hadin kai da hakuri a tsakanin al’ummomi daban-daban don samun zaman lafiya da ci gaban Jihar Gombe da kasa baki daya, yana mai bayyana zaman lafiya a matsayin ginshilin ci gaban zamantakewa da tattalin arzikin kowace al’umma.

 

Gwamna Inuwa, ya kuma jaddada cewa gwamnatin sa ba za ta lamunci duk wani abu da zai iya kawo cikas ga zaman lafiya da ake da shi a jihar ba, kuma zata ci gaba da mai da hankali wajen ganin an samar da ribar demokradiyya ga al’ummar Jihar.

 

Sai ya yi kiran yin addu’o’i na musamman ga shugabanni a kowane mataki. “A irin wannan muhimmin lokaci na sauyin mulki da za a yi a kasar mu nan bada dadewa ba, ina kira a gare mu dukka, mu yi ta addu’a domin samun sauyin cikin kwanciyar hankali, musamman ma ga shugabanni masu zuwa a mukamai daban-daban, domin Allah ya basu hikima ya kuma yi musu jagora wajen sauke nauyin da ke kan su”.

 

“Ina mika godiya ta ga sarakuna da shugabannin al’umma da malaman addini da kuma dokacin al’ummar Jihar Gombe bisa goyon bayan da suke bai wa gwamnatin mu. Ina kira a gare mu, da mu sake sadaukar da kan mu, mu bada kyakkywar gudumawa ga ci gaban jihar mu. Ina mai tabbatar muku cewa gwamnatin mu ta himmatu wajen ganin Jihar Gombe ta samu ci gaba cikin sauri da kuma dorewar ci gabanta baki daya.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Manyan Labarai

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano
Manyan Labarai

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 
Labarai

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025
Next Post
Sin Da Zambia Sun Yi Bikin Cika Shekaru 60 Da Fara Tura Likitocin Sin Afirka

Sin Da Zambia Sun Yi Bikin Cika Shekaru 60 Da Fara Tura Likitocin Sin Afirka

LABARAI MASU NASABA

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

October 31, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025
Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

October 31, 2025
Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

October 31, 2025
Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.