ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Inuwa Ya Bukaci Musulmai Su Ci Gaba Da Habbaka Darussan Ramadana

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Inuwa

Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ya buƙaci al’ummar jihar su ci gaba da gudanar da ayyukan su na ibadah da suka yi a watan na Ramadana, da addu’o’in zaman lafiya da ci gaban jihar da Nijeriya baki daya. 

 

Gwamnan ya yi wannan kiran ne a sakon sa na Barka da Sallah da Ismaila Uba Misilli, hadiminsa a bangaren yada labarai da hulda da jama’a ya fitar.

ADVERTISEMENT
  • Inuwa Ya Bai Wa ‘Yan Kasuwan Gombe Kyautar Naira Miliyan 500 Don Karfafa Kasuwancinsu 

Gwamna Inuwa, wadda ya bayyana sallar Eid-el-Fitr a matsayin lokacin tunani da nazari kan rahamomin Allah ga bayi, ya bukaci al’ummar Musulmi su rinka dabbaƙa darusan da suka koya a watan na Ramadan a rayuwar su ta yau da kullum.

 

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Ya ce, “Yayin da muke bukukuwan Eid-el-Fitr, ina yi mana nasiha da mu yi koyi da kyawawan darussa na watan Ramadan wadanda suke nuni da takawa, da biyayya, da sadaukarwa. Dole ne dukkan mu mu yi koyi da koyarwar Musulunci da ke tabbatar da zaman lafiya da hakuri, da kana’a da kuma kauna”.

 

Gwamna Inuwa ya kuma bukaci al’ummar jihar da cewa kar su sare game da kalubalen zamantakewa da na tattalin arziƙin da ake fuskanta a kasar nan, amma su jajirce wajen yin addu’o’i, yana mai cewa idan suka jajirce, jarabawar da ake ciki za ta wuce, kuma Nijeriya za ta kara karfi da karsashi da hadin kai.

 

Ya kuma bukaci jama’a su ci gaba da ririta zaman lafiya da kwanciyar hankali da ake da shi a jihar, inda ya yi kira ga malamai da sarakuna su ci gaba da wa’azin hadin kai da hakuri a tsakanin al’ummomi daban-daban don samun zaman lafiya da ci gaban Jihar Gombe da kasa baki daya, yana mai bayyana zaman lafiya a matsayin ginshilin ci gaban zamantakewa da tattalin arzikin kowace al’umma.

 

Gwamna Inuwa, ya kuma jaddada cewa gwamnatin sa ba za ta lamunci duk wani abu da zai iya kawo cikas ga zaman lafiya da ake da shi a jihar ba, kuma zata ci gaba da mai da hankali wajen ganin an samar da ribar demokradiyya ga al’ummar Jihar.

 

Sai ya yi kiran yin addu’o’i na musamman ga shugabanni a kowane mataki. “A irin wannan muhimmin lokaci na sauyin mulki da za a yi a kasar mu nan bada dadewa ba, ina kira a gare mu dukka, mu yi ta addu’a domin samun sauyin cikin kwanciyar hankali, musamman ma ga shugabanni masu zuwa a mukamai daban-daban, domin Allah ya basu hikima ya kuma yi musu jagora wajen sauke nauyin da ke kan su”.

 

“Ina mika godiya ta ga sarakuna da shugabannin al’umma da malaman addini da kuma dokacin al’ummar Jihar Gombe bisa goyon bayan da suke bai wa gwamnatin mu. Ina kira a gare mu, da mu sake sadaukar da kan mu, mu bada kyakkywar gudumawa ga ci gaban jihar mu. Ina mai tabbatar muku cewa gwamnatin mu ta himmatu wajen ganin Jihar Gombe ta samu ci gaba cikin sauri da kuma dorewar ci gabanta baki daya.”

Inuwa
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Sin Da Zambia Sun Yi Bikin Cika Shekaru 60 Da Fara Tura Likitocin Sin Afirka

Sin Da Zambia Sun Yi Bikin Cika Shekaru 60 Da Fara Tura Likitocin Sin Afirka

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.