ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Inuwa Ya Bukaci Musulmai Su Ci Gaba Da Habbaka Darussan Ramadana

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Inuwa

Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ya buƙaci al’ummar jihar su ci gaba da gudanar da ayyukan su na ibadah da suka yi a watan na Ramadana, da addu’o’in zaman lafiya da ci gaban jihar da Nijeriya baki daya. 

 

Gwamnan ya yi wannan kiran ne a sakon sa na Barka da Sallah da Ismaila Uba Misilli, hadiminsa a bangaren yada labarai da hulda da jama’a ya fitar.

ADVERTISEMENT
  • Inuwa Ya Bai Wa ‘Yan Kasuwan Gombe Kyautar Naira Miliyan 500 Don Karfafa Kasuwancinsu 

Gwamna Inuwa, wadda ya bayyana sallar Eid-el-Fitr a matsayin lokacin tunani da nazari kan rahamomin Allah ga bayi, ya bukaci al’ummar Musulmi su rinka dabbaƙa darusan da suka koya a watan na Ramadan a rayuwar su ta yau da kullum.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

Ya ce, “Yayin da muke bukukuwan Eid-el-Fitr, ina yi mana nasiha da mu yi koyi da kyawawan darussa na watan Ramadan wadanda suke nuni da takawa, da biyayya, da sadaukarwa. Dole ne dukkan mu mu yi koyi da koyarwar Musulunci da ke tabbatar da zaman lafiya da hakuri, da kana’a da kuma kauna”.

 

Gwamna Inuwa ya kuma bukaci al’ummar jihar da cewa kar su sare game da kalubalen zamantakewa da na tattalin arziƙin da ake fuskanta a kasar nan, amma su jajirce wajen yin addu’o’i, yana mai cewa idan suka jajirce, jarabawar da ake ciki za ta wuce, kuma Nijeriya za ta kara karfi da karsashi da hadin kai.

 

Ya kuma bukaci jama’a su ci gaba da ririta zaman lafiya da kwanciyar hankali da ake da shi a jihar, inda ya yi kira ga malamai da sarakuna su ci gaba da wa’azin hadin kai da hakuri a tsakanin al’ummomi daban-daban don samun zaman lafiya da ci gaban Jihar Gombe da kasa baki daya, yana mai bayyana zaman lafiya a matsayin ginshilin ci gaban zamantakewa da tattalin arzikin kowace al’umma.

 

Gwamna Inuwa, ya kuma jaddada cewa gwamnatin sa ba za ta lamunci duk wani abu da zai iya kawo cikas ga zaman lafiya da ake da shi a jihar ba, kuma zata ci gaba da mai da hankali wajen ganin an samar da ribar demokradiyya ga al’ummar Jihar.

 

Sai ya yi kiran yin addu’o’i na musamman ga shugabanni a kowane mataki. “A irin wannan muhimmin lokaci na sauyin mulki da za a yi a kasar mu nan bada dadewa ba, ina kira a gare mu dukka, mu yi ta addu’a domin samun sauyin cikin kwanciyar hankali, musamman ma ga shugabanni masu zuwa a mukamai daban-daban, domin Allah ya basu hikima ya kuma yi musu jagora wajen sauke nauyin da ke kan su”.

 

“Ina mika godiya ta ga sarakuna da shugabannin al’umma da malaman addini da kuma dokacin al’ummar Jihar Gombe bisa goyon bayan da suke bai wa gwamnatin mu. Ina kira a gare mu, da mu sake sadaukar da kan mu, mu bada kyakkywar gudumawa ga ci gaban jihar mu. Ina mai tabbatar muku cewa gwamnatin mu ta himmatu wajen ganin Jihar Gombe ta samu ci gaba cikin sauri da kuma dorewar ci gabanta baki daya.”

Inuwa
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Next Post
Sin Da Zambia Sun Yi Bikin Cika Shekaru 60 Da Fara Tura Likitocin Sin Afirka

Sin Da Zambia Sun Yi Bikin Cika Shekaru 60 Da Fara Tura Likitocin Sin Afirka

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.