• English
  • Business News
Saturday, June 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matashi Ya Shiga Hannu Kan Yi Wa ‘Yar Shekara 4 Fyade A Nasarawa

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
Matashi Ya Shiga Hannu Kan Yi Wa ‘Yar Shekara 4 Fyade A Nasarawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar tsaron farin kaya ta (NSCDC) a Jihar Nasarawa ta kama wani mai suna Ibrahim Hashimu mai shekaru 18 bisa zargin lalata da karamar yarinya mai shekaru 4 da haihuwa.

Kakakin hukumar NSCDC, DSC Jerry Victor ne, ya bayyana hakan a wata tattaunawa ta musamman da manema labarai a ranar Juma’a a garin Lafiya.

  • Zaben Shugabannin Majalisa Ta 10: Ko Tarihi Zai Maimaita Kansa?
  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Hakimi A Zamfara

Ya bayyana cewa lamarin ya faru ne a ranar 22 ga watan Afrilu, 2023 a Angwan Magaji, kusa da fadar Sarkin Lafia.

Acewarsa, an ga waddda abin ya shafa na kuka da sannan tana zubar da jini a jikinta.

An ruwaito ta bayyana wa mahaifiyarta yadda lamarin ya faru.

Labarai Masu Nasaba

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai

Kakakin ya kara da cewa da samun wannan labari nan take rundunar ta dauki matakin gaggauwa kuma ana cikin haka ne aka kama wanda ake zargin Ibrahim Hashimu aka kai ofishin NSCDC domin amsa tambayoyi.

Ya ce wanda ake zargin ya amsa laifin aikata laifin kuma ya roki a yi masa afuwa.

A halin da ake ciki kuma, rundunar da ke yaki da barna a jihar tare da ‘yan sandan Nasarawa Eggon, sun cafke wasu ‘yan ta’adda guda uku da ake zargi da lalata igiyar wutar lantarki mai karfin 33kV a tashar Mada da ke karamar hukumar Nasarawa Eggon.

Mutanen ukun da aka kama sun hada da Yakubu Ossan mai shekaru 55 da Mustapha Ibrahim mai shekaru 24 da kuma Hussain Yakubu dan shekara 21.

Rundunar ‘yansandan ta kuma ce ta kama Aisha Saidu ‘yar shekara 22 bisa rahotannin da ta ke cewa ta ci zarafin ‘ya’yanta a garin Lafia babban birnin jihar.

“An ga raunuka a ko ina a jikin wadanda abin ya shafa da aka garzaya da su wurin likita don kula da lafiyarsu,” in ji kakakin.

Ya ce ana ci gaba da gudanar da bincike bayan haka za a gurfanar da wadanda ake zargin.

Kwamandan NSCDC, Abbas Bappa Muhammed, a lokacin da yake kokawa kan yadda ake lalata kananan yara, fyade a jihar, ya ce hakki ne kan kowa na kars yara mata, yana mai kira ga al’ummar jihar da iyaye da su sanya ido sosai kan yaransu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FyadeMatashiNasarawaYarinya
ShareTweetSendShare
Previous Post

UEFA Za Ta Fito Da Tsarin Mafi Karancin Albashin ‘Yan Kwallo A Turai

Next Post

Cutar Maleriya Ta Kashe Mutum 290,000 A Duniya A Cikin Shekara Biyu

Related

jam'iyyu
Rahotonni

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

6 hours ago
Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai

7 hours ago
Nijeriya Da Morocco Za Su Sanya Hannu Kan Kulla Yarjejeniyar Aikin Bututun Iskar Gas
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Himmatu Wajen Inganta Karfin Sashen Fetur Da Gas Na Cikin Gida

8 hours ago
Gwamnati Ta Yi Karin Haske Kan Biyan Tallafin Rage Radadi Da Mafi Karancin Albashi
Labarai

Gwamnati Ta Yi Karin Haske Kan Biyan Tallafin Rage Radadi Da Mafi Karancin Albashi

10 hours ago
Dawanau
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dukufa Wajen Karya Farashin Kayan Abinci – Minista

12 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Shahararren Ɗan Damfarar Yanar Gizo A Bauchi
Labarai

Ƴansanda Sun Kama Shahararren Ɗan Damfarar Yanar Gizo A Bauchi

13 hours ago
Next Post
Cutar Maleriya Ta Kashe Mutum 290,000 A Duniya A Cikin Shekara Biyu

Cutar Maleriya Ta Kashe Mutum 290,000 A Duniya A Cikin Shekara Biyu

LABARAI MASU NASABA

Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin

Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin

June 13, 2025
jam'iyyu

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

June 13, 2025
Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai

Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai

June 13, 2025
Babban Jami’in Diflomasiyyar Kasar Sin Ya Yi Kiran Karfafa Alaka Da Afirka

Babban Jami’in Diflomasiyyar Kasar Sin Ya Yi Kiran Karfafa Alaka Da Afirka

June 13, 2025
Xi Ya Yi Kira Da A Kara Azamar Gina Kasa A Gabar Da Ake Bikin Cika Shekaru 120 Da Haihuwar Dan Mazan Jiya Chen Yun

Xi Ya Yi Kira Da A Kara Azamar Gina Kasa A Gabar Da Ake Bikin Cika Shekaru 120 Da Haihuwar Dan Mazan Jiya Chen Yun

June 13, 2025
Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi

Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi

June 13, 2025
Nijeriya Da Morocco Za Su Sanya Hannu Kan Kulla Yarjejeniyar Aikin Bututun Iskar Gas

Gwamnatin Tarayya Ta Himmatu Wajen Inganta Karfin Sashen Fetur Da Gas Na Cikin Gida

June 13, 2025
Bin Hanya Daya Da Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Muhimmin Mataki Ne Na Ba Da Tabbaci Ga Huldar Ciniki Da Tattalin Arzikin Sin Da Amurka

Bin Hanya Daya Da Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Muhimmin Mataki Ne Na Ba Da Tabbaci Ga Huldar Ciniki Da Tattalin Arzikin Sin Da Amurka

June 13, 2025
Sin Ta Bayyana Adawa Da Keta Hurumin ‘Yanci Tsaro Da Ikon Mulkin Yankunan Iran

Sin Ta Bayyana Adawa Da Keta Hurumin ‘Yanci Tsaro Da Ikon Mulkin Yankunan Iran

June 13, 2025
Gwamnati Ta Yi Karin Haske Kan Biyan Tallafin Rage Radadi Da Mafi Karancin Albashi

Gwamnati Ta Yi Karin Haske Kan Biyan Tallafin Rage Radadi Da Mafi Karancin Albashi

June 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.