• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Aikin Ceto Muka Zo Yi, Inji Zaɓaɓɓen Gwamnan Zamfara Yayin Ƙaddamar Da Kwamitin Karbar Mulki

by yahuzajere
2 years ago
in Labarai
0
Aikin Ceto Muka Zo Yi, Inji Zaɓaɓɓen Gwamnan Zamfara Yayin Ƙaddamar Da Kwamitin Karbar Mulki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yau Talata, Zaɓaɓɓen gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya ƙaddamar da kwamitin karɓar mulki mai membobi 60, inda ya ƙara jaddada cewa ya zo aikin ceto ne tare da sake gina Zamfara.

Kwamitin mai membobi 60 a ƙarƙashin jagorancin tsohon Sufeto Janar na ‘yan sanda, M.D Abubakar, an kaddamar da shi ne a Gusau, babban birnin jihar.

Sanarwar manema labarai da ofishin zababben gwamnan ya fitar dauke da rattaba hannun, Sulaiman Bala Idris, ta bayyana cewa, da yake jawabi a wajen ƙaddamar da kwamitin, Dauda Lawal, ya ce nauyin da ya rataya a kan kwamitin shi ne gudanar da shirye-shiryen da suka dace domin karɓar mulki cikin kwanciyar hankali a jihar Zamfara.

Ya bayyana kwamitin mai membobi 60 a matsayin taron ƙwararru da ke da gogewar shekaru a ɓangarori daban-daban, waɗanda aka zaɓo su cikin tsanaki domin shiga cikin tsarin karɓar mulkin.

  • Ina Da Yakinin Samun Nasara A Kotu -Dan Takarar Gwamnan APC A Bauchi

“Canjin da al’ummar Zamfara suka zaɓa, canji ne daga rashin tsaro, rayuwar talauci, zuwa rayuwa ta tsaro, wadata da walwala, riƙon amana, da mutunta doka.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

“Kwamitin amsar mulkin mai membobi 60 an kafa shi ne da nufin fara dukkanin shirye-shiryen da ya kamata tare da kuma tsara yadda za a samu sauyi cikin sauƙi na sabuwar gwamnatinmu a jihar wanda zai fara aiki a ranar 29 ga Mayu, 2023.

“An ɗorawa kwamitin alhakin samar da ingantaccen tsarin haɗin gwiwa da samar da hanyar sadarwa ta yau da kullum da Gwamnati mai barin gado tare da kuma karɓar ragamar gudanarwar gwamnati mai zuwa domin samun nasarar karɓar mulkin.

“Kwamitin zai kuma haɗa hannu da ma’aikatu, rassa da kuma hukumomi, sannan zai duba kuɗaɗen gwamnati mai barin gado tare da mai da hankali kan rasiɗai, ƙadarori, da kuma lamuni da sauransu.

“Al’ummar jihar Zamfara na da kyakkyawan fata; sun zaɓe mu ne cike da imanin za mu iya ceto tare da sake gina jiharmu.

“Mun kuma zaɓe ku a matsayin membobin kwamitin karɓar mulki saboda mun yi imanin cewa tsawon shekarun gogewarku da ƙwarewar ku, za mu iya aza harsashi ga gwamnati mai jiran gado domin ta yi nasara kan aikin ceton da ta sa gaba.

“Da wannan taƙaitaccen bayani da kuma yardar Allah, a halin yanzu, nake ƙaddamar da wannan kwamitin na karɓar mulki.”

A ranar 29 ga Mayun 2023 ne ake sa ran rantsar da sabon zababben gwamnan a Gusau babban birnin Jihar Zamfara.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bagudu Ya Shiga Tsakani Kan Rikicin KAEDCO Da Sojoji

Next Post

Sin Za Ta Karfafa Kare Namun Daji Karkashin Sabuwar Dokar Da Aka Kaddamar

Related

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya
Labarai

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

7 hours ago
Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025
Labarai

Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

8 hours ago
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin
Labarai

Hukumar NRC Ta Dakatar Da Zirga-zirgar Jiragen Kasa Na Abuja zuwa Kaduna

9 hours ago
Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara
Manyan Labarai

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

11 hours ago
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin
Manyan Labarai

Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

13 hours ago
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba
Da ɗumi-ɗuminsa

Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

17 hours ago
Next Post
Sin Za Ta Karfafa Kare Namun Daji Karkashin Sabuwar Dokar Da Aka Kaddamar

Sin Za Ta Karfafa Kare Namun Daji Karkashin Sabuwar Dokar Da Aka Kaddamar

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

August 26, 2025
Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

August 26, 2025
Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

August 26, 2025
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

August 26, 2025
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Hukumar NRC Ta Dakatar Da Zirga-zirgar Jiragen Kasa Na Abuja zuwa Kaduna

August 26, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

August 26, 2025
Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

August 26, 2025
Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

August 26, 2025
Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

August 26, 2025
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.