• English
  • Business News
Thursday, May 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yawon Bude Ido Na Hutun Ranar ‘Yan Kwadago A Kasar Sin Zai Ingiza Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Yawon Bude Ido Na Hutun Ranar ‘Yan Kwadago A Kasar Sin Zai Ingiza Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu rahotanni na cewa, tattalin arzikin duniya zai samu tagomashi daga tafiye tafiyen yawon bude ido da Sinawa za su gudanar zuwa kasashen waje, a lokacin hutun ranar ‘yan kwadago ta bana, daya daga cikin lokutan hutu mafiya tsayi a kasar Sin.

A bana Sinawa masu tarin yawa sun shirya ziyartar wurare da dama, a karon farko bayan shafe shekaru 3 ana aiwatar da tsauraran matakan yaki a annobar COVID a cikin kasar, wanda hakan ya haifar da takaituwar tafiye tafiye. Kaza lika bikin na bana, na gudana ne tun daga ranar 29 ga watan Afirilu zuwa 3 ga watan Mayun nan. Shi ne kuma biki mafi tsayi na farko da ake yi a kasar, tun bayan sake bude zirga zirga ta rukunonin masu fita yawon shakatawa daga kasar a watan Fabarairun da ya gabata.

  • Sin Za Ta Karfafa Kare Namun Daji Karkashin Sabuwar Dokar Da Aka Kaddamar

A cewar hukumar lura da harkokin yawan shakatawa ta MDD, Sinawa masu yawon bude ido ne ke kan gaba a duniya, wajen bunkasa kasuwar kasa da kasa a fannin, inda yayin tafiye-tafiye da suka gudanar zuwa ketare, tsakanin shekarun 2015 zuwa 2019, suka kashe kimanin dalar Amurka biliyan 260 a kowace shekara.

Alkaluman shahararren kamfanin samar da hidimomin tafiye tafiye na kasar Sin Ctrip, sun nuna adadin masu duba tikitin jiragen sama a wannan lokaci ya karu da ninki 9, sama da na makamancin lokaci na bara, kuma masu neman hidimomin tafiye-tafiye zuwa ketare sun karu da ninki 18.

Har ila yau, wani rahoto daga kamfanin tantance alkaluma game da harkokin kasuwanni da cinikayya na Euromonitor International, ya nuna cewa, karuwar adadin masu tafiye tafiyen na wannan karo, ya zo a gabar da hada hadar sayayya ke kara fadada a kasar Sin.

Labarai Masu Nasaba

Sin Na Maraba Da Kamfanonin Kasa Da Kasa Har Da Na Amurka 

Hadin Gwiwar Sin Da Yankin Turai Na Kara Kawo Haske Ga Tattalin Arzikin Duniya

Rahoton ya ce bisa matsakaicin hasashe, Sinawa masu fita yawon bude ido na kashe kudaden da suka ninka na shekarar 2019 har sau biyu. Ana hasashen Sinawa masu tafiya yawon shakatawa za su zamo a sahun gaba, a fannin samar da kudaden shiga, ga kantuna marasa dora haraji kan hajojin su, a jimillar fannoni 6 cikin 10 na kasuwanni mafiya muhimmanci, matakin da zai samar da harajin sayayya da darajar sa za ta kai kimanin dalar Amurka biliyan 117. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Rundunar ‘Yan Sanda Sun Cafke Dan Yahoo Da Ya Kware Kan Cutar ‘Yan Kasar Hungary A Nijeriya

Next Post

Zaɓaɓɓen Gwamnan Zamfara Ya Ziyarci Kasuwar Da Aka Yi Gobara A Gusau

Related

Sin Na Maraba Da Kamfanonin Kasa Da Kasa Har Da Na Amurka 
Daga Birnin Sin

Sin Na Maraba Da Kamfanonin Kasa Da Kasa Har Da Na Amurka 

14 hours ago
Hadin Gwiwar Sin Da Yankin Turai Na Kara Kawo Haske Ga Tattalin Arzikin Duniya
Daga Birnin Sin

Hadin Gwiwar Sin Da Yankin Turai Na Kara Kawo Haske Ga Tattalin Arzikin Duniya

15 hours ago
Yunkurin Philippines Bai Kai Gaci Ba A Tekun Kudancin Kasar Sin 
Daga Birnin Sin

Yunkurin Philippines Bai Kai Gaci Ba A Tekun Kudancin Kasar Sin 

16 hours ago
Kamfanoni Mallakin Gwamnatin Sin Sun Samu Bunkasa Bisa Daidaito Cikin Watanni Hudu Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Kamfanoni Mallakin Gwamnatin Sin Sun Samu Bunkasa Bisa Daidaito Cikin Watanni Hudu Na Farkon Bana

17 hours ago
Masu Bincike Na Sin Sun Cimma Sabon Sakamako A Fannin Saurin Sadarwa Tsakanin Tauraron Dan Adam Da Doron Duniya
Daga Birnin Sin

Masu Bincike Na Sin Sun Cimma Sabon Sakamako A Fannin Saurin Sadarwa Tsakanin Tauraron Dan Adam Da Doron Duniya

19 hours ago
An Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Taron Kolin ASEAN-Sin-GCC
Daga Birnin Sin

An Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Taron Kolin ASEAN-Sin-GCC

19 hours ago
Next Post
Zaɓaɓɓen Gwamnan Zamfara Ya Ziyarci Kasuwar Da Aka Yi Gobara A Gusau

Zaɓaɓɓen Gwamnan Zamfara Ya Ziyarci Kasuwar Da Aka Yi Gobara A Gusau

LABARAI MASU NASABA

Zaman lafiya

MDD Ta Gudanar Da Bikin Ranar Tunawa Da Dakarun Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Duniya Ta 2025

May 29, 2025
Buhari Ya Yabi Tinubu, Ya Bukaci ‘Yan Nijeriya Su Rage Tsammani Da Dogon Buri

Buhari Ya Yabi Tinubu, Ya Bukaci ‘Yan Nijeriya Su Rage Tsammani Da Dogon Buri

May 29, 2025
Gwamnatin Kano Ta Fara Biyan Tsoffin Kansiloli Na APC Sama Da Naira Biliyan 16

Gwamnatin Kano Ta Fara Biyan Tsoffin Kansiloli Na APC Sama Da Naira Biliyan 16

May 29, 2025
Sin Na Maraba Da Kamfanonin Kasa Da Kasa Har Da Na Amurka 

Sin Na Maraba Da Kamfanonin Kasa Da Kasa Har Da Na Amurka 

May 28, 2025
Miƙa Mulki Daga Buhari Zuwa Tinubu: Abubuwan Da Suka Fi Jan Hankali

Tinubu Ya Yi Ƙoƙari, Gyaran Nijeriya Aikin Kowa Da Kowa Ne – Buhari

May 28, 2025
Hadin Gwiwar Sin Da Yankin Turai Na Kara Kawo Haske Ga Tattalin Arzikin Duniya

Hadin Gwiwar Sin Da Yankin Turai Na Kara Kawo Haske Ga Tattalin Arzikin Duniya

May 28, 2025
Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi

Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi

May 28, 2025
Yunkurin Philippines Bai Kai Gaci Ba A Tekun Kudancin Kasar Sin 

Yunkurin Philippines Bai Kai Gaci Ba A Tekun Kudancin Kasar Sin 

May 28, 2025
Babu Wata Sauran Mafaka Ga ‘Yan Ta’adda, In Ji Shugaban Rundunar Sojin Sama

Babu Wata Sauran Mafaka Ga ‘Yan Ta’adda, In Ji Shugaban Rundunar Sojin Sama

May 28, 2025
Kamfanoni Mallakin Gwamnatin Sin Sun Samu Bunkasa Bisa Daidaito Cikin Watanni Hudu Na Farkon Bana

Kamfanoni Mallakin Gwamnatin Sin Sun Samu Bunkasa Bisa Daidaito Cikin Watanni Hudu Na Farkon Bana

May 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.