ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yawon Bude Ido Na Hutun Ranar ‘Yan Kwadago A Kasar Sin Zai Ingiza Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya

by CMG Hausa
3 years ago

Wasu rahotanni na cewa, tattalin arzikin duniya zai samu tagomashi daga tafiye tafiyen yawon bude ido da Sinawa za su gudanar zuwa kasashen waje, a lokacin hutun ranar ‘yan kwadago ta bana, daya daga cikin lokutan hutu mafiya tsayi a kasar Sin.

A bana Sinawa masu tarin yawa sun shirya ziyartar wurare da dama, a karon farko bayan shafe shekaru 3 ana aiwatar da tsauraran matakan yaki a annobar COVID a cikin kasar, wanda hakan ya haifar da takaituwar tafiye tafiye. Kaza lika bikin na bana, na gudana ne tun daga ranar 29 ga watan Afirilu zuwa 3 ga watan Mayun nan. Shi ne kuma biki mafi tsayi na farko da ake yi a kasar, tun bayan sake bude zirga zirga ta rukunonin masu fita yawon shakatawa daga kasar a watan Fabarairun da ya gabata.

  • Sin Za Ta Karfafa Kare Namun Daji Karkashin Sabuwar Dokar Da Aka Kaddamar

A cewar hukumar lura da harkokin yawan shakatawa ta MDD, Sinawa masu yawon bude ido ne ke kan gaba a duniya, wajen bunkasa kasuwar kasa da kasa a fannin, inda yayin tafiye-tafiye da suka gudanar zuwa ketare, tsakanin shekarun 2015 zuwa 2019, suka kashe kimanin dalar Amurka biliyan 260 a kowace shekara.

ADVERTISEMENT

Alkaluman shahararren kamfanin samar da hidimomin tafiye tafiye na kasar Sin Ctrip, sun nuna adadin masu duba tikitin jiragen sama a wannan lokaci ya karu da ninki 9, sama da na makamancin lokaci na bara, kuma masu neman hidimomin tafiye-tafiye zuwa ketare sun karu da ninki 18.

Har ila yau, wani rahoto daga kamfanin tantance alkaluma game da harkokin kasuwanni da cinikayya na Euromonitor International, ya nuna cewa, karuwar adadin masu tafiye tafiyen na wannan karo, ya zo a gabar da hada hadar sayayya ke kara fadada a kasar Sin.

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Rahoton ya ce bisa matsakaicin hasashe, Sinawa masu fita yawon bude ido na kashe kudaden da suka ninka na shekarar 2019 har sau biyu. Ana hasashen Sinawa masu tafiya yawon shakatawa za su zamo a sahun gaba, a fannin samar da kudaden shiga, ga kantuna marasa dora haraji kan hajojin su, a jimillar fannoni 6 cikin 10 na kasuwanni mafiya muhimmanci, matakin da zai samar da harajin sayayya da darajar sa za ta kai kimanin dalar Amurka biliyan 117. (Saminu Alhassan)

CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
Zaɓaɓɓen Gwamnan Zamfara Ya Ziyarci Kasuwar Da Aka Yi Gobara A Gusau

Zaɓaɓɓen Gwamnan Zamfara Ya Ziyarci Kasuwar Da Aka Yi Gobara A Gusau

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.