• English
  • Business News
Tuesday, September 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

KAEDCO Za Ta Dawo Da Wutar Lantarki Cikin Sa’o’i Kadan A Jihar Kebbi – SSG 

by Sulaiman and Umar Faruk
2 years ago
in Labarai
0
KAEDCO Za Ta Dawo Da Wutar Lantarki Cikin Sa’o’i Kadan A Jihar Kebbi – SSG 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kamfanin rarraba Wutar Lantarki ta Kaduna, KAEDCO, ya amince ya maido da wutar lantarki a cikin Birnin Kebbi cikin wasu sa’o’i kadan nan gaba.

Hakan ya biyo bayan sa baki da Gwamnan Jihar Kebbi Sanata Abubakar Atiku Bagudu ya yi na sasanta rikicin da ke tsakanin kamfanin da Sojojin Nijeriya.

  • Bagudu Ya Shiga Tsakani Kan Rikicin KAEDCO Da Sojoji

Sakataren gwamnatin jihar, Alhaji Babale Umar Yauri ne ya sanar da hakan bayan wata ganawa da mahukuntan KAEDCO da shugabannin rundunar sojin da sauran shugabannin hukumomin tsaro a ofishinsa da ke Birnin Kebbi.

Gwamnan ya umarci SSG da a samar da zaman lafiya tsakanin bangarorin biyu da ke rikici da juna wanda zai share fagen maido da wutar lantarki ga mazauna babban birnin jihar.

Da yake zantawa da manema labarai bayan kammala taron, Babale Umar Yauri a madadin gwamnatin jihar Kebbi ya nemi afuwar hukumar ta KAEDCO a kan abin da ya samu ma’aikatansu, tare da yin Allah wadai da irin halin da suke ciki, yana mai ba da tabbacin gwamnati da jami’an tsaro za su samar da ingantaccen tsaro ga ma’aikatan kamfanin don gudanar da ayyukansu a cikin jihar.

Labarai Masu Nasaba

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Mutum 9 Da Harsasai 4,264 Da Muggan Makamai A Nasarawa 

Babu Shirin Gaggawa Wajen Fara Aiwatar Da Harajin Kashi 5 Na Man Fetur – Minista

Hakazalika SSG ya jaddada cewa kwamandan rundunar a Birnin Kebbi bai baiwa wani soja izinin rike ma’aikatan KAEDCO ba ballantana ya goyi bayan abin da ya faru, domin sojoji ba sa amince wa da ayyukan rashin bin doka da oda ba.

Sakataren gwamnati ya yi kira ga al’ummar jihar da su ci gaba da bin doka da oda, inda ya ce duk ma’aikacin KAEDCO da aka samu yana gudanar da ayyukansa ba bisa ka’ida ba a kai rahoto ga mahukuntan kamfanin domin daukar matakin ladabtarwa.

Ya bayyana karara cewa Gwamna Abubakar Atiku Bagudu zai ci gaba da ba da tallafin kayan aiki ga KAEDCO don tabbatar da samar da wutar lantarki akai-akai a duk sassan jihar Kebbi.

Haka Kuma ya godewa jami’an KAEDCO bisa yadda suka magance rikicin tare da nuna jin dadinsu ga jami’an soji da suka shawo kan lamarin cikin gaggawa.

A nasa jawabin, shugaban yankin KAEDCO mai kula da jihohin Sokoto, Kebbi da Zamfara, Mista Sunday Yahaya, ya yaba da fatan alheri da hakuri da gwamnatin jihar Kebbi ta yi kan wannan mummunan lamari.

Mista Sunday Yahaya ya kuma ba da hakuri cewa lamarin ya koma ga wannan matakin, amma ya yi kira ga jama’a da su ba ma’aikatan kamfanin hadin kai wajen gudanar da ayyukansu.

Shugaban yankin na KAEDCO yayin da ya umarci dukkan ma’aikatansu da su koma bakin aiki cikin gaggawa, ya shawarci masu amfani da wutar lantarki da su kai rahoton ma’aikatan KAEDCO da suka yi kura-kurai ga hukumomin da suka dace, inda ya tabbatar da cewa kamfanin yana da tsarin ladabtar da ma’aikatansa.

Taron wanda SSG ya jagoranta ya samu halartar mukaddashin shugaban ma’aikata na jihar Alhaji Safiyanu Garba Bena da wakilin kwamishinan ‘yan sanda, kwamandan rundunar sojojin na Birnin Kebbi, Kwamandan Bataliya Light Tank Battalion 223, Zuru, Wakilin Kwanturolan Kwastam, da Ma’aikatan Gudanarwa na KAEDCO.

A karshen taron bangarorin uku da aka yi tsakanin gwamnatin jihar da shugaban hukumar KAEDCO da wasu zababbun hukumomin tsaro, an rattaba hannu kan wani kudiri da dukkanin bangarorin da abin ya shafa suka sanya hannu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnati Ta Janye Tuhumar Rashawa Ta Naira Biliyan 1.84 Kan Mataimakin Dasuki Da EFCC Ke Yi Masa

Next Post

Kwararun Kasa Da Kasa: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Zaburar Da Mutane Da Yawa A Duniya

Related

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Mutum 9 Da Harsasai 4,264 Da Muggan Makamai A Nasarawa 
Labarai

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Mutum 9 Da Harsasai 4,264 Da Muggan Makamai A Nasarawa 

1 hour ago
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN
Labarai

Babu Shirin Gaggawa Wajen Fara Aiwatar Da Harajin Kashi 5 Na Man Fetur – Minista

3 hours ago
MDD Ta Yi Allah-wadai Da Harin Boko Haram A Bama
Manyan Labarai

MDD Ta Yi Allah-wadai Da Harin Boko Haram A Bama

5 hours ago
Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba
Ra'ayi Riga

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

6 hours ago
APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami
Manyan Labarai

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

7 hours ago
Ana Zargin Jami’in Sibil Difens Da Harbe Abokin Aikinsa A Abuja
Labarai

Ana Zargin Jami’in Sibil Difens Da Harbe Abokin Aikinsa A Abuja

10 hours ago
Next Post
Kwararun Kasa Da Kasa: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Zaburar Da Mutane Da Yawa A Duniya

Kwararun Kasa Da Kasa: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Zaburar Da Mutane Da Yawa A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

September 9, 2025
Nazarin CGTN: Cin Gajiyar Damarmaki Tare Da Samun Sakamakon Moriyar Juna Ta Hanyar Yin Komai A Bude

Nazarin CGTN: Cin Gajiyar Damarmaki Tare Da Samun Sakamakon Moriyar Juna Ta Hanyar Yin Komai A Bude

September 9, 2025
Kasar Sin Ta Samar Da Kaso 30 Na Jimillar Kason Ci Gaban Masana’antun Duniya A Tsakanin 2021 Zuwa 2025

Kasar Sin Ta Samar Da Kaso 30 Na Jimillar Kason Ci Gaban Masana’antun Duniya A Tsakanin 2021 Zuwa 2025

September 9, 2025
Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Mutum 9 Da Harsasai 4,264 Da Muggan Makamai A Nasarawa 

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Mutum 9 Da Harsasai 4,264 Da Muggan Makamai A Nasarawa 

September 9, 2025
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Babu Shirin Gaggawa Wajen Fara Aiwatar Da Harajin Kashi 5 Na Man Fetur – Minista

September 9, 2025
Xi Ya Aike Da Martanin Wasika Ga Wakilan Malamai Na Musamman Don Karfafa Musu Gwiwa

Xi Ya Aike Da Martanin Wasika Ga Wakilan Malamai Na Musamman Don Karfafa Musu Gwiwa

September 9, 2025
MDD Ta Yi Allah-wadai Da Harin Boko Haram A Bama

MDD Ta Yi Allah-wadai Da Harin Boko Haram A Bama

September 9, 2025
Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

September 9, 2025
APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

September 9, 2025
Ana Zargin Jami’in Sibil Difens Da Harbe Abokin Aikinsa A Abuja

Ana Zargin Jami’in Sibil Difens Da Harbe Abokin Aikinsa A Abuja

September 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.