ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

KAEDCO Za Ta Dawo Da Wutar Lantarki Cikin Sa’o’i Kadan A Jihar Kebbi – SSG 

by Sulaiman and Umar Faruk
3 years ago
KAEDCO

Kamfanin rarraba Wutar Lantarki ta Kaduna, KAEDCO, ya amince ya maido da wutar lantarki a cikin Birnin Kebbi cikin wasu sa’o’i kadan nan gaba.

Hakan ya biyo bayan sa baki da Gwamnan Jihar Kebbi Sanata Abubakar Atiku Bagudu ya yi na sasanta rikicin da ke tsakanin kamfanin da Sojojin Nijeriya.

  • Bagudu Ya Shiga Tsakani Kan Rikicin KAEDCO Da Sojoji

Sakataren gwamnatin jihar, Alhaji Babale Umar Yauri ne ya sanar da hakan bayan wata ganawa da mahukuntan KAEDCO da shugabannin rundunar sojin da sauran shugabannin hukumomin tsaro a ofishinsa da ke Birnin Kebbi.

ADVERTISEMENT

Gwamnan ya umarci SSG da a samar da zaman lafiya tsakanin bangarorin biyu da ke rikici da juna wanda zai share fagen maido da wutar lantarki ga mazauna babban birnin jihar.

Da yake zantawa da manema labarai bayan kammala taron, Babale Umar Yauri a madadin gwamnatin jihar Kebbi ya nemi afuwar hukumar ta KAEDCO a kan abin da ya samu ma’aikatansu, tare da yin Allah wadai da irin halin da suke ciki, yana mai ba da tabbacin gwamnati da jami’an tsaro za su samar da ingantaccen tsaro ga ma’aikatan kamfanin don gudanar da ayyukansu a cikin jihar.

LABARAI MASU NASABA

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

Hakazalika SSG ya jaddada cewa kwamandan rundunar a Birnin Kebbi bai baiwa wani soja izinin rike ma’aikatan KAEDCO ba ballantana ya goyi bayan abin da ya faru, domin sojoji ba sa amince wa da ayyukan rashin bin doka da oda ba.

Sakataren gwamnati ya yi kira ga al’ummar jihar da su ci gaba da bin doka da oda, inda ya ce duk ma’aikacin KAEDCO da aka samu yana gudanar da ayyukansa ba bisa ka’ida ba a kai rahoto ga mahukuntan kamfanin domin daukar matakin ladabtarwa.

Ya bayyana karara cewa Gwamna Abubakar Atiku Bagudu zai ci gaba da ba da tallafin kayan aiki ga KAEDCO don tabbatar da samar da wutar lantarki akai-akai a duk sassan jihar Kebbi.

Haka Kuma ya godewa jami’an KAEDCO bisa yadda suka magance rikicin tare da nuna jin dadinsu ga jami’an soji da suka shawo kan lamarin cikin gaggawa.

A nasa jawabin, shugaban yankin KAEDCO mai kula da jihohin Sokoto, Kebbi da Zamfara, Mista Sunday Yahaya, ya yaba da fatan alheri da hakuri da gwamnatin jihar Kebbi ta yi kan wannan mummunan lamari.

Mista Sunday Yahaya ya kuma ba da hakuri cewa lamarin ya koma ga wannan matakin, amma ya yi kira ga jama’a da su ba ma’aikatan kamfanin hadin kai wajen gudanar da ayyukansu.

Shugaban yankin na KAEDCO yayin da ya umarci dukkan ma’aikatansu da su koma bakin aiki cikin gaggawa, ya shawarci masu amfani da wutar lantarki da su kai rahoton ma’aikatan KAEDCO da suka yi kura-kurai ga hukumomin da suka dace, inda ya tabbatar da cewa kamfanin yana da tsarin ladabtar da ma’aikatansa.

Taron wanda SSG ya jagoranta ya samu halartar mukaddashin shugaban ma’aikata na jihar Alhaji Safiyanu Garba Bena da wakilin kwamishinan ‘yan sanda, kwamandan rundunar sojojin na Birnin Kebbi, Kwamandan Bataliya Light Tank Battalion 223, Zuru, Wakilin Kwanturolan Kwastam, da Ma’aikatan Gudanarwa na KAEDCO.

A karshen taron bangarorin uku da aka yi tsakanin gwamnatin jihar da shugaban hukumar KAEDCO da wasu zababbun hukumomin tsaro, an rattaba hannu kan wani kudiri da dukkanin bangarorin da abin ya shafa suka sanya hannu.

KAEDCO
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
  • Sulaiman
    Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
  • Sulaiman
    Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
  • Sulaiman
    Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy
KAEDCO
Umar Faruk
+ posts Bio
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnatin Kebbi Ta Amince Da ₦2.07bn Alawus-alawus Ga Ma’aikatan Manyan Makarantu
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Maye Gurbin Mataimakinsa Da Ibrahim Augie A Zaɓen 2027
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Matashi Ya Shiga Hannu Kan Zargin Wulaƙanta Alƙur’ani A Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Miƙa Yara 5 Da Aka Ceto Daga Hannun Masu Safarar Mutane Ga Iyayensu

MASU ALAKA

Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato
Manyan Labarai

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu
Rahotonni

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara
Labarai

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Next Post
Kwararun Kasa Da Kasa: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Zaburar Da Mutane Da Yawa A Duniya

Kwararun Kasa Da Kasa: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Zaburar Da Mutane Da Yawa A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.