ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bagudu Ya Shiga Tsakani Kan Rikicin KAEDCO Da Sojoji

by Abubakar Abba
3 years ago
Bagudu

Gwamnan Jihar Kebbi Abubakar Atiku Bagudu, ya umarci sakataren gwamnatin jihar, Babale Umar Yauri, ya shiga tsakani kan rikicin da ya auku a makon da ya wuce tsakanin sojoji da ma’aikatan kamfanin samar wutar lantarki (KAEDCO) kan yanke wutar da ya shiga kwana uku a Birnin Kebbi.

Bagudu ya bayyana hakan ne a jiya Litinin a yayin da yake jawabi dakin taro da ke masaukin da ake sauke shugaban kasa da ke a Birnin Kebbi.

  • Kwamandan Yaki Da ‘Yan Sara-Suka Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Zamfara
  • Zazzabin Lassa Ya Yi Ajalin Mutum 154 A Nijeriya —NCDC

Ya ce, kamfanin ba zai iya gudanar da aikinsa idan masu amfani da wutar ba sa biyan kudin wutar da suka yi amfani da ita ba, inda ya kara da cewa, hakan zai zama abu mai wuya a samar da wutar mai dorewa a jihar.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “A baya muna samar da rangwame ga masu amfani da wutar, amma yanzu mun kai wani lokaci da ba za mu iya ci gaba da yin hakan domin muna samo kudaden ne daga cibiyoyi daban-daban.”

Tun a ranar Asabar din da ra gabata ne, kamfanin na KAEDCO ya yanke wutar da yake tura wa daukacin Birnin Kebbi saboda rikicin.

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

An ruwaito cewa, umarnin na gwamnan da ya bai wa sakataren gwamnatin jihar, ana sa ran zai tattauna a Barikin Dukku da mahukuntan kamfanin na KAEDCO da kuma mahukuntan sojin domin a lalubo mafita kan rikicin da ya janyo rashin samar da wutar a daukacin fadin babban birinin jihar.

Bugu da kari, wani babban jami’in soji da ke a Barikin Dukku a Birnin Kebbi wanda kuma ya nemi a sakaya sunansa ya ce, sojojin da suka je kamfanin na KAEDCO, ba su doki ma’aikaci ko daya ba.

A cewarsa, sojojin sun je kamfanin ne kawai domin su shigar da korafi da nuna bacin ransu kan rashin samar da wuta da kamfanin ke yi, inda hakan ya lalata kayan da matansu ke yin sana’a wanda sai da wutar ne za su iya gudanar sa sana’arsu.

Bagudu
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
Aikin Ceto Muka Zo Yi, Inji Zaɓaɓɓen Gwamnan Zamfara Yayin Ƙaddamar Da Kwamitin Karbar Mulki

Aikin Ceto Muka Zo Yi, Inji Zaɓaɓɓen Gwamnan Zamfara Yayin Ƙaddamar Da Kwamitin Karbar Mulki

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.