• English
  • Business News
Sunday, October 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Batun Daurarru 3,298 Masu Jiran Hukuncin Kisa A Nijeriya

by Abdulrazaq Yahuza
2 years ago
Daurarru

Batun cunkoson Gidajen Gyara Hali a fadin Nijeriya na ci gaba da zama cikin abubuwan tattaunawa a wurare da dama na harkokin al’umma a fadin kasar nan. Ga wadanda basu san cikakken halin da gidajen yarin suke ciki ba, har yanzu su na nan a halin da turawan mulkin mallaka suka samar da su a shekarun baya kafin su koma kasashen su da sunan bamu ‘yancin kai. Chanza sunan su daga yadda aka san su a da tunda farko na ‘Nigerian Prison Serbice (NPS)’ zuwa ‘Nigerian Correctional Serbice’ bai nuna wani canji daga yadda aka san su a daba a cikin tsarin hukunce-hukuncen shari’a na Nijeriya.

A farko an tsara zaunar da daurarru masu laifi 50,000 ne a gidajen gyaran halin amma a halin yanzu gidajen yarin kasar nan na dauke ne da masu laifi fiye da mutum 73,000.

  • An Gabatar Da Rahoton Bincike Kan Harin Da CIA Ta Kai Ga Sauran Kasashe Ta Yanar Gizo

Tabbas wannan cunkoson ya haifar da matsaloli da daman gaske wadanda suka hada da rashin tsafta, rashin samun kulawa ta magunguna ga marasa lafiya da kuma yadda ake samun karuwa cututtuka da kuma yadda daurarrau ke kara kangarewa bayan sun fito daga wadannan gidajen gyaran halin fiye da yadda suka shiga tunda farko.

Amma kuma cikin manya-manyan matsalolin da ake fuskanta su ta na yadda ake samun karuwar daurarun da ke jiran hukuncin kisa. Kwanaki Hukumar Kula da Gidajen Gyaran halin ta fitar da bayanin cewa a halin yanzu akwai fiye da mutum 3,298 da ke jiran a yanke musu hukuncin kisa a gidajen yari daban-daban a fadin kasar nan. Jami’in Watsa Labaran Hukumar, Abubakar Umar, ya bayyana cewa, ba a cika gaggauta zartar da hukuncin kisa ba da zaran an yanke ba.

Ya kara da cewa, ana daukar dogon lokaci a saboda yadda ake samun daukaka karar hukuncin da aka yanke a manyan kotuna.

LABARAI MASU NASABA

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

“Wasu masu laifin kan yi jiran fiye da shrekara 15 kafin a yanke musu hukuncin. Suna nan suna jiran a zo a yanke musu hukuncin kisan kamar yadda kotu ta yanke. Muna na da su da dama, a yanzu a kwai mutum 3,298 da ke jiran hukuncin kisa. Su ne kusan kashi 4.5 na yawan daurarrun da muke da su a gidajen gyaran hali a fadin kasar nan,” in ji shi.
Tabbas hukuncin kisa wani abu ne da aka ci gaba da takaddama a kai, wasu na ganin alfanunsa wasu kuma na ganin bashi da wani amfani a tsarin ladaftar da rayuwar al’umma suna kuma kira da a gaggauta soke shi gaba daya.
Ra’ayin wannan jaridar a nan shi ne, duk kuwa da ra’ayin da wani yake da shi a kan hukuncin kisan, a bayyana yake cewa, bai kamata a bar daurarrau masu jiran hukuncin kisa su dauki dogon lokaci suna jiran a yanke musu hukucin ba, wannan ba a bin da za a amince da shi ba ne.
A lokutta da dama a barin dauraru masu jiran hukuncin kisa su dade na tsawon sherkaru ba tare da da sanin halin da suke ciki ba, wannan rashin adalci ne garesu da iyalansu da kuma al’umma gaba daya.
Daya daga cikin abin da ke haifar da wadannan matsalolin shi ne kin gwamnoni na sanya hannu a takardar hukuncin zartar da hukuncin kisan. Amma a yanzu wasu gwamnoni da dama suna jinkirin sanya hannu a kan takardar hukuncin kisan saboda abubuwan da suka shafi siyasa da sauransu. Wannan ya sanya dauraru da ke jiran hukuncin kisa suke ci gaba da zaman jiran dirshan ba tare da sanin yaushe za a yanke musu hukuncin ba.
Ida za a iya tunawan tun da aka dawo mulkin farar hula a shekara 1999, gwamnoni 2 ne kawai suka sanya hannu a kan zartar da hukuncin kisa ga daurarru na fadin kasar nan.
Za kuma a iya tunawa da cewa, tsohon gwamnan Jihar Kano, Ibrahim Shekarau ne na farko da ya sanya hannu a zartar da hukuncin kisa a shekarar 2006, yayin da Gwamna Adams Oshiomhole ya zama na biyu a shekarar 2012.
Tsohon gwamnan Kano ya zartar da hukuncin kisan wasu dauraru ne da ake jiran hukuncin kisa a inda aka zartar musu da hukuncin ba tare da bata lokaci ba, yayin Oshiomhole ya sa hannu a kisan mutum biyu a jiharsa ta Edo.
Yayin da za a iya amincewa da ana iya samun gwamnonin da suke adawa da hukuncin kisa amma ya kuma kamata a fahimci cewa, tuni kotu ta samu wadannna mutanen da laifukkan da ake zargin da su kuma ta yanke musu hukuncin na kisa.
A ra’ayinmu, kin sanya hannu a hukuncin kisan da gwamnoni suke kin yi kamar suna danne hukucin kotuna ke nan wanda hakan kuma yana nuna suka katsalandan ga hurumin kotunan ke nan. Wannan kuma ba adalci ne ba ga daurarun kuma yana nuna cewa, za a iya amfani da karefin siyasa wajen canza hukunce-hukuncen da kotuna suke yankewa a kasar nan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Tsaro

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja
Tsaro

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Next Post
‘Yan Nijeriya 376 Aka Kwaso Daga Sudan – Minista Sadiya

'Yan Nijeriya 376 Aka Kwaso Daga Sudan - Minista Sadiya

LABARAI MASU NASABA

gombe

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

October 18, 2025
ASUU

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025
Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.