• English
  • Business News
Wednesday, June 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zababbun Sanatocin APC Na Arewa Ta Tsakiya Sun Ki Amincewa Da Mukaman Shiyya

by Abubakar Abba
2 years ago
in Labarai
0
Shirin APC Na Zabar Sabon Kakakin Majalisar Wakilai Ya Tada Kura
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Zababbun Sanatocin da suka fito daga Arewa ta Tsakiya a karkashin jam’iyyu daban-daban, sun nuna rashin amincewa da mukaman shiyya da jam’iyyar APC ta sanar.

APC a shirin da ta yi, ta sahale wa Sanata Godswill Akpabio da ya fito daga shiyyar Kudu Maso Kudu ya zama shugaban majalisar dattawa a majalisar ta 10, inda kuma Sanata Barau Jibrin, daga Arewa Maso Yamma zai zama mataimakinsa.

  • ‘Yansanda Sun Hallaka ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato Bindigogi A Zamfara
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Benuwe

Haka zalika, a majalisar wakilai kuwa APC ta sahalewaTajudeen Abass daga Arewa Maso Yamma da ya zama shugaban majalisar wakilai, inda Benjamin Kalu daga Kudu Maso Gabas zai zama mataimakinsa.

Hakan ya tilasta wa zababbun Sanatocin da suka fito daga Arewa Maso Tsakiya rubuta wa shugaban APC na kasa Abdullahi Adamu wasika, inda suka sanar masa da kin lamunta da matsayin na APC ta kasa.

Sun bayyana cewa, a cikin wannan tsarin, ba a sanya Arewa ta Tsakiya a ciki ba duk da cewa zababben shugaban kasa da mataimakinsa, ba daga shiyyar suka fito ba.

Labarai Masu Nasaba

DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Neja Ta Soke Hawan Sallah Sakamakon Ambaliyar Ruwan Mokwa

Wasikar mai taken: matsayar da yan majalisa suka cimma kan shugabancin majalisa ta 10 kan shugabancin shiyya.

Sanatoci 18 ne suka rattaba hannu kan wasikar wadanda suka hada da, Sanata Mohammed Sani Musa daga Neja ta Gabas, Sanata Ashiru Oyelola Yisa daga Kwara ta Kudu, Sanata Sadiq Umar Suleiman daga Kwara ta Arewa, Sanata Mustapha Saliu daga Kwara ta Tsakiya da kuma Sanata Isah Jibrin daga Kogi ta Gabas.

Sauran su ne, Sanata Abba Moro daga Benuwe ta Kudu, Sanata Godiya Akwashiki daga Nasarawa ta Arewa, Sanata Ahmed Aliyu Wadada daga Nasarawa ta Yamma, Sanata Ireti Kingibe daga Birnin Tarayya, Sanata Sunday Karimi Steve daga Kogi ta Yamma, Sanata Sadiku Abubakar daga Kogi ta Tsakiya da kuma Sanata Peter Ndalikali Jiya daga Neja ta Kudu.

Har ila yau, sun kuma hada da Sanata Napoleon Binkap Bali daga Filato ta Kudu, Sanata Mwadkion Simon Davou daga Filato ta Arewa, Sanata Diket Plang daga Filato ta Tsakiya, Sanata Mohammed O. Onawo daga Nasarawa ta Kudu, Sanata Emmanuel M. Udende daga Benuwe ta Gabas da kuma Sanata Titus Tartenger Zam daga Benuwe ta Yamma.

Wasikar ta ce, mu Sanatocin da muka fito daga Arewa ta Tsakiya mun gudanar da ganawa a ranar 8 ga watan Mayu 2023, inda a ganawar ne, muka cimma wannan matsaya, cewar shiyyarmu ta jima tana tabbatar da ci gaban siyasa a kasar nan kuma za ta ci gaba da yin hakan tare da ci gaba da goya wa zababben shugaban kasa baya.

A cewar wasikar shiyyar ta kuma samawar wa APC kuri’u kashi 41 a zaben shugaban kasa na ranar 25 ga watan Fabirairu, saboda haka, ita ma shiyyar lokaci ya yi da za a rama mata.

Bisa wadanan hujojin, muna kira ga APC ta kasa da ta gaggauta janye matsayar da ta cimma kan tsarin mukaman shugabancin majalisar ta 10.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCShugabanciTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yansanda Sun Hallaka ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato Bindigogi A Zamfara

Next Post

Kawu Sumaila Ya Gargadi Tinubu Kan Yi Wa Majalisa Katsa-Landan

Related

DSS
Labarai

DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja

2 hours ago
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Neja Ta Soke Hawan Sallah Sakamakon Ambaliyar Ruwan Mokwa

3 hours ago
katsina
Labarai

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Hadin Gwiwa Da ‘Yan Kasuwa Domin Cigaban Jihar

4 hours ago
Ambaliya: Gwamna Zulum Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Agaji A Borno
Manyan Labarai

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

6 hours ago
Sanusi
Manyan Labarai

‘Yansanda A Kano Sun GargaÉ—i Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

17 hours ago
Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 
Labarai

Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

19 hours ago
Next Post
Kawu Sumaila Ya Gargadi Tinubu Kan Yi Wa Majalisa Katsa-Landan

Kawu Sumaila Ya Gargadi Tinubu Kan Yi Wa Majalisa Katsa-Landan

LABARAI MASU NASABA

DSS

DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja

June 4, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Neja Ta Soke Hawan Sallah Sakamakon Ambaliyar Ruwan Mokwa

June 4, 2025
katsina

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Hadin Gwiwa Da ‘Yan Kasuwa Domin Cigaban Jihar

June 4, 2025
Ambaliya: Gwamna Zulum Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Agaji A Borno

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

June 4, 2025
Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

June 3, 2025
Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

June 3, 2025
Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

June 3, 2025
Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

June 3, 2025
Sanusi

‘Yansanda A Kano Sun GargaÉ—i Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

June 3, 2025
Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

June 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.