ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zababbun Sanatocin APC Na Arewa Ta Tsakiya Sun Ki Amincewa Da Mukaman Shiyya

by Abubakar Abba
3 years ago
APC

Zababbun Sanatocin da suka fito daga Arewa ta Tsakiya a karkashin jam’iyyu daban-daban, sun nuna rashin amincewa da mukaman shiyya da jam’iyyar APC ta sanar.

APC a shirin da ta yi, ta sahale wa Sanata Godswill Akpabio da ya fito daga shiyyar Kudu Maso Kudu ya zama shugaban majalisar dattawa a majalisar ta 10, inda kuma Sanata Barau Jibrin, daga Arewa Maso Yamma zai zama mataimakinsa.

  • ‘Yansanda Sun Hallaka ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato Bindigogi A Zamfara
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Benuwe

Haka zalika, a majalisar wakilai kuwa APC ta sahalewaTajudeen Abass daga Arewa Maso Yamma da ya zama shugaban majalisar wakilai, inda Benjamin Kalu daga Kudu Maso Gabas zai zama mataimakinsa.

ADVERTISEMENT

Hakan ya tilasta wa zababbun Sanatocin da suka fito daga Arewa Maso Tsakiya rubuta wa shugaban APC na kasa Abdullahi Adamu wasika, inda suka sanar masa da kin lamunta da matsayin na APC ta kasa.

Sun bayyana cewa, a cikin wannan tsarin, ba a sanya Arewa ta Tsakiya a ciki ba duk da cewa zababben shugaban kasa da mataimakinsa, ba daga shiyyar suka fito ba.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Wasikar mai taken: matsayar da yan majalisa suka cimma kan shugabancin majalisa ta 10 kan shugabancin shiyya.

Sanatoci 18 ne suka rattaba hannu kan wasikar wadanda suka hada da, Sanata Mohammed Sani Musa daga Neja ta Gabas, Sanata Ashiru Oyelola Yisa daga Kwara ta Kudu, Sanata Sadiq Umar Suleiman daga Kwara ta Arewa, Sanata Mustapha Saliu daga Kwara ta Tsakiya da kuma Sanata Isah Jibrin daga Kogi ta Gabas.

Sauran su ne, Sanata Abba Moro daga Benuwe ta Kudu, Sanata Godiya Akwashiki daga Nasarawa ta Arewa, Sanata Ahmed Aliyu Wadada daga Nasarawa ta Yamma, Sanata Ireti Kingibe daga Birnin Tarayya, Sanata Sunday Karimi Steve daga Kogi ta Yamma, Sanata Sadiku Abubakar daga Kogi ta Tsakiya da kuma Sanata Peter Ndalikali Jiya daga Neja ta Kudu.

Har ila yau, sun kuma hada da Sanata Napoleon Binkap Bali daga Filato ta Kudu, Sanata Mwadkion Simon Davou daga Filato ta Arewa, Sanata Diket Plang daga Filato ta Tsakiya, Sanata Mohammed O. Onawo daga Nasarawa ta Kudu, Sanata Emmanuel M. Udende daga Benuwe ta Gabas da kuma Sanata Titus Tartenger Zam daga Benuwe ta Yamma.

Wasikar ta ce, mu Sanatocin da muka fito daga Arewa ta Tsakiya mun gudanar da ganawa a ranar 8 ga watan Mayu 2023, inda a ganawar ne, muka cimma wannan matsaya, cewar shiyyarmu ta jima tana tabbatar da ci gaban siyasa a kasar nan kuma za ta ci gaba da yin hakan tare da ci gaba da goya wa zababben shugaban kasa baya.

A cewar wasikar shiyyar ta kuma samawar wa APC kuri’u kashi 41 a zaben shugaban kasa na ranar 25 ga watan Fabirairu, saboda haka, ita ma shiyyar lokaci ya yi da za a rama mata.

Bisa wadanan hujojin, muna kira ga APC ta kasa da ta gaggauta janye matsayar da ta cimma kan tsarin mukaman shugabancin majalisar ta 10.

APC
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Next Post
Kawu Sumaila Ya Gargadi Tinubu Kan Yi Wa Majalisa Katsa-Landan

Kawu Sumaila Ya Gargadi Tinubu Kan Yi Wa Majalisa Katsa-Landan

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.