• English
  • Business News
Saturday, October 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wani Mutum Ya Kashe Mahaifiyarsa Kan Naira 10,000

by Khalid Idris Doya
2 years ago

Wani mutum da aka bayyana sunansa da Osaro Owate, ya shiga hannun hukumar ‘yansandan jihar Ribas bisa zargin kashe mahaifiyarsa a kauyen Alesa da ke karamar hukumar Eleme kan rashin jituwar da ta shiga tsakaninsu kan naira dubu goma (N10,000) kacal.

Wanda ake zargin, ya yi ikirarin cewa ya na fama da matsalar gaulanci ko tsatstsauran ra’ayin addini na tsawon sama da shekara 30, ya amsa da bakinsa kan cewa ya kashe mamar tasa da fartanya ne.

  • Amurka Ba Za Ta Cimma Yunkurin Taron Dangi Bisa Fakewa Da Batun Taiwan Ba

Da yake magana ta cikin wani faifayin bidiyon da ya yadu sosai a Soshal Midiya, Owate ya ce, ya bukaci naira dubu ashirin (N20,000) a wajen marigayiyar mamar tasa domin ya sayi kayan sawa da zan yi adon zuwa wajen bisne wata gawa, amma sai ta ba shi naira 10 kacal, kuma hakan ya kasa masa matuka

Wanda ake zargin ya ce, “Jiya (Ranar Juma’a), na fada mata zuwa safiyar Asabar ta ciro kudin da za ta bani da zan sanyi kayan sanyawa domin halartar bikin biso. Da safiyar yau din kafin na tashi sai ya zama ita ta kama shirye-shiryen fita daga gida domin ta je ta halarci bikin biso.

“Na tambayeta maganar kudin da na bukata daga wajenta na ce ko dai ba ta son na halarci wajen bison ne kuma. Sai ta ce to bari za ta ciro min kudin.

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NASENI

Daɓid Adeyemi

“Ta tafi ta je ta ciro N20,000 da muka hadu sai ta dauko N10,000 kacal ta ba ni. Na sha mamakin a inane zan samu kayan dubu goma na saya.

“Da na kama binta, sai ta fara musguna min da zagina wai sa’o’ina su na aiki su na sana’a don meye ni nake zaman banza bana sana’ar komai. Na tunatar da ita cewa ina fama da matsalar da ke damuna ta yaya zan je na nemi aiki alhalin ina da matsala.?

“Amma duk da hakan ta cigaba da surfamin fada kawai sai na bugeta da fartanya. Tana kicin domin dafa abinci ne lokacin da na buga mata fartanya. Da na fusata matuka, kawai sai na gama da ita. Idan ni ma rayuwata za ta kawo karshe don na yi hakan ba damuwa na mutun kawai na shirya ma hakan. Ina fama da matsalar gaulanci sama da shekara 30. Kamar yadda kuke kallona yanzu ina son na mutum.”

Har zuwa lokacin hada wannan rahoton rundunar ‘yansandan jihar Ribas ba ta fitar da wani bayani a kai ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Labarai

Hukumar NASENI

October 25, 2025
Labarai

Daɓid Adeyemi

October 25, 2025
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka
Kiwon Lafiya

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

October 25, 2025
Next Post
NDLEA Ta Kwace Maganin Cutar Hauka Mai Nauyin Kilo 150 A Gombe

NDLEA Ta Cafke Mutane 218 Kan Zargin Safarar Miyagun Kwayoyi Masu Nauyin Kilo 5,610 A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NASENI

October 25, 2025
An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

October 25, 2025

Daɓid Adeyemi

October 25, 2025
Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

October 25, 2025
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

October 25, 2025
Kasar Sin Ta Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Na 15

Kasar Sin Ta Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Na 15

October 25, 2025
Gwarzon Mai Koyar Da Wasanni Na Shekarar 2025 Justine Madugu

Gwarzon Mai Koyar Da Wasanni Na Shekarar 2025 Justine Madugu

October 25, 2025
An Kaddamar Da Nuna Muhimman Shirye-shiryen CMG A Membobin APEC

An Kaddamar Da Nuna Muhimman Shirye-shiryen CMG A Membobin APEC

October 25, 2025
Zuwan Tsoffin ’Yan Wasan Barcelona Abuja Ya Nuna Ana Samun Zaman Lafiya A Nijeriya – Matawalle

Zuwan Tsoffin ’Yan Wasan Barcelona Abuja Ya Nuna Ana Samun Zaman Lafiya A Nijeriya – Matawalle

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Ma’aikacin Lafiya Na Shekarar 2025 Dakta Seidu Adebayo Bello

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.