ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wani Mutum Ya Kashe Mahaifiyarsa Kan Naira 10,000

by Khalid Idris Doya
3 years ago

Wani mutum da aka bayyana sunansa da Osaro Owate, ya shiga hannun hukumar ‘yansandan jihar Ribas bisa zargin kashe mahaifiyarsa a kauyen Alesa da ke karamar hukumar Eleme kan rashin jituwar da ta shiga tsakaninsu kan naira dubu goma (N10,000) kacal.

Wanda ake zargin, ya yi ikirarin cewa ya na fama da matsalar gaulanci ko tsatstsauran ra’ayin addini na tsawon sama da shekara 30, ya amsa da bakinsa kan cewa ya kashe mamar tasa da fartanya ne.

  • Amurka Ba Za Ta Cimma Yunkurin Taron Dangi Bisa Fakewa Da Batun Taiwan Ba

Da yake magana ta cikin wani faifayin bidiyon da ya yadu sosai a Soshal Midiya, Owate ya ce, ya bukaci naira dubu ashirin (N20,000) a wajen marigayiyar mamar tasa domin ya sayi kayan sawa da zan yi adon zuwa wajen bisne wata gawa, amma sai ta ba shi naira 10 kacal, kuma hakan ya kasa masa matuka

ADVERTISEMENT

Wanda ake zargin ya ce, “Jiya (Ranar Juma’a), na fada mata zuwa safiyar Asabar ta ciro kudin da za ta bani da zan sanyi kayan sanyawa domin halartar bikin biso. Da safiyar yau din kafin na tashi sai ya zama ita ta kama shirye-shiryen fita daga gida domin ta je ta halarci bikin biso.

“Na tambayeta maganar kudin da na bukata daga wajenta na ce ko dai ba ta son na halarci wajen bison ne kuma. Sai ta ce to bari za ta ciro min kudin.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

“Ta tafi ta je ta ciro N20,000 da muka hadu sai ta dauko N10,000 kacal ta ba ni. Na sha mamakin a inane zan samu kayan dubu goma na saya.

“Da na kama binta, sai ta fara musguna min da zagina wai sa’o’ina su na aiki su na sana’a don meye ni nake zaman banza bana sana’ar komai. Na tunatar da ita cewa ina fama da matsalar da ke damuna ta yaya zan je na nemi aiki alhalin ina da matsala.?

“Amma duk da hakan ta cigaba da surfamin fada kawai sai na bugeta da fartanya. Tana kicin domin dafa abinci ne lokacin da na buga mata fartanya. Da na fusata matuka, kawai sai na gama da ita. Idan ni ma rayuwata za ta kawo karshe don na yi hakan ba damuwa na mutun kawai na shirya ma hakan. Ina fama da matsalar gaulanci sama da shekara 30. Kamar yadda kuke kallona yanzu ina son na mutum.”

Har zuwa lokacin hada wannan rahoton rundunar ‘yansandan jihar Ribas ba ta fitar da wani bayani a kai ba.

Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ‘Yansanda Sun Cafke Tsoho Mai Shekara 70 Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 8 Fyaɗe A Bauchi

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
NDLEA Ta Kwace Maganin Cutar Hauka Mai Nauyin Kilo 150 A Gombe

NDLEA Ta Cafke Mutane 218 Kan Zargin Safarar Miyagun Kwayoyi Masu Nauyin Kilo 5,610 A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.