Kasar Sin, ta yi kira ga Amurka da kasashen yammacin duniya, su gaggauta soke takunkuman da suka yi gaban kansu wajen kakabawa, da dakatar da keta hakkokin jama’a a wasu kasashe.
Wakilin na Sin ne ya yi kiran a jiya, yayin zama na 50 na majalisar kare hakkin dan Adam ta MDD, a lokacin da yake halartar tattaunawar da aka yi tsakanin wasu masana masu zaman kansu, a bangren hakkokin bil adama da hadin giwar kasashen duniya. (Fa’iza)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp