• English
  • Business News
Saturday, July 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Matashi Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 10 Fyade A Bauchi

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Takaddama Kan Shirin Daukar Sabbin ‘Yansanda
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani matashi mai shekara 33 a duniya, ana zarginsa da yin amfani da sinadarin da ke sanya maye wajen gusar da hankalin wata karamar yarinya ‘yar shekara 10, tare da yi mata fyade a karamar hukumar Ningi a Jihar Bauchi.

Matashin wanda ya yaudari yarinyar ta hanyar ba ta lemo da ake zargin na dauke da sinadarin da ke sanya maye domin samun damar lalata da ita ba tare da saninta ba.

  • Tinubu Ya Nada Akume Da Femi A Sakataren Gwamnati Da Shugaban Ma’aikatan Fadarsa
  • Tinubu Ya Shiga Wata Ganawa Da Gwamnonin Jam’iyyar APC A Abuja

A cewar wata sanarwar manema labarai da kakakin ‘yansandan Jihar Bauchi, SP Ahmed Mohammed Wakil ya fitar a ranar Juma’a, ya ce, wanda ake zargin ya samu damar fyade da yarinyar ne ta hanyar amfani da karfin tsiya.

Ya ce, “A ranar 25 ga watan Mayun 2023, wani mutum da ke kauyen Nasaru a karamar hukumar Ningi ya kai rahoto caji ofis din ‘yansandan Ningi, inda ya ce wani matashi da suke gari daya ya yaudari ‘yarsa mai shekara 10 ta hanyar ba ta lemo da ake zargin na dauke da sinadarin da ke sanya maye wanda hakan ya sanya hankalinta ya gushe.

“Ya yi amfani da wannan damar ya yi mata fyade, wanda ya hakan ya sanya yariyar ta gamu da raunuka a al’aurarta kana ta yi ta zubar da jini.”

Labarai Masu Nasaba

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

A fadin sanarwar, tun lokacin da suka amshi rahoton, tawagarsu cikin hanzari suka garzaya inda lamarin ya faru tare da daukar yarinyar zuwa babban asibitin Ningi daga bisani aka sauya mata wurin jinya zuwa asibitin kula da masu yoyon fitsari (NOFIC) da ke Ningi, bayan kaurin jikinta aka sake nausawa da ita zuwa asibitin gwamnatin tarayya (FMC) da ke Birnin Kudu a jihar Jigawa domin neman kulawar likitoci.

A cewar Wakil, tun lokacin ‘yansanda suka sha alwashin sai sun cafko wanda ya aikata hakan domin tabbatar da yarinyar ta samua adalcin da ya dace ta samu, “Kan hakan mun cafke wanda ake zargi, Danladi Ibrahim.

“A lokacin da ake tuhumarsa, ya amsa da kansa cewa ya aikata laifin, don haka bincike na cigaba da guduna da zarar aka kammala za mu gurfanar da shi a gaban kuliya.”

Daga bisani rundunar ‘yansandan ta jawo hankalin al’umma da cewa suke sanya ido da lura da yankunansu domin dakile aniyar bata gari a kowani lokaci tare da gaggawar kai rahoton faruwar lamuran da ba daidai ba cikin hanzari domin daukan matakan gaggawa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'YansandaBauchiFyadeMatashiYarinya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Ya Nada Akume Da Femi A Sakataren Gwamnati Da Shugaban Ma’aikatan Fadarsa

Next Post

Kungiyar Kwadago Za Ta Shiga Yajin Aiki Kan Cire Tallafin Man Fetur

Related

An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

59 minutes ago
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

2 hours ago
Abin Da Ya Sa ‘Yan Nijeriya Ba Su Mori Dimokuradiyya Ba Har Yanzu –Jega
Labarai

Shirin Tinubu Kan Kiwon Dabbobi Zai Samar Da Ayyukan Yi Miliyan 5 Ga Matasa – Jega

4 hours ago
‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote
Labarai

‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote

5 hours ago
Ku Zama Cikin Shirin Samun Sauyin Yanayi – NiMet
Labarai

Ku Zama Cikin Shirin Samun Sauyin Yanayi – NiMet

13 hours ago
Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya
Ra'ayi Riga

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

17 hours ago
Next Post
Kungiyar Kwadago Za Ta Shiga Yajin Aiki Kan Cire Tallafin Man Fetur

Kungiyar Kwadago Za Ta Shiga Yajin Aiki Kan Cire Tallafin Man Fetur

LABARAI MASU NASABA

An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

July 5, 2025
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

July 5, 2025
Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya

Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya

July 5, 2025
Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci

Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci

July 5, 2025
Abin Da Ya Sa ‘Yan Nijeriya Ba Su Mori Dimokuradiyya Ba Har Yanzu –Jega

Shirin Tinubu Kan Kiwon Dabbobi Zai Samar Da Ayyukan Yi Miliyan 5 Ga Matasa – Jega

July 5, 2025
Ana Tuhumar Tsohon Ɗan Wasan Arsenal Thomas Partey Da Laifin Fyaɗe A Ƙasar Ingila

Ana Tuhumar Tsohon Ɗan Wasan Arsenal Thomas Partey Da Laifin Fyaɗe A Ƙasar Ingila

July 5, 2025
‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote

‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote

July 5, 2025
In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba

In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba

July 4, 2025
Sin Za Ta Gaggauta Aikin Raya Sana’o’in Samar Da Wutar Lantarki Daga Zafin Rana

Sin Za Ta Gaggauta Aikin Raya Sana’o’in Samar Da Wutar Lantarki Daga Zafin Rana

July 4, 2025
Ku Zama Cikin Shirin Samun Sauyin Yanayi – NiMet

Ku Zama Cikin Shirin Samun Sauyin Yanayi – NiMet

July 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.