ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Matashi Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 10 Fyade A Bauchi

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Fyade

Wani matashi mai shekara 33 a duniya, ana zarginsa da yin amfani da sinadarin da ke sanya maye wajen gusar da hankalin wata karamar yarinya ‘yar shekara 10, tare da yi mata fyade a karamar hukumar Ningi a Jihar Bauchi.

Matashin wanda ya yaudari yarinyar ta hanyar ba ta lemo da ake zargin na dauke da sinadarin da ke sanya maye domin samun damar lalata da ita ba tare da saninta ba.

  • Tinubu Ya Nada Akume Da Femi A Sakataren Gwamnati Da Shugaban Ma’aikatan Fadarsa
  • Tinubu Ya Shiga Wata Ganawa Da Gwamnonin Jam’iyyar APC A Abuja

A cewar wata sanarwar manema labarai da kakakin ‘yansandan Jihar Bauchi, SP Ahmed Mohammed Wakil ya fitar a ranar Juma’a, ya ce, wanda ake zargin ya samu damar fyade da yarinyar ne ta hanyar amfani da karfin tsiya.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “A ranar 25 ga watan Mayun 2023, wani mutum da ke kauyen Nasaru a karamar hukumar Ningi ya kai rahoto caji ofis din ‘yansandan Ningi, inda ya ce wani matashi da suke gari daya ya yaudari ‘yarsa mai shekara 10 ta hanyar ba ta lemo da ake zargin na dauke da sinadarin da ke sanya maye wanda hakan ya sanya hankalinta ya gushe.

“Ya yi amfani da wannan damar ya yi mata fyade, wanda ya hakan ya sanya yariyar ta gamu da raunuka a al’aurarta kana ta yi ta zubar da jini.”

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Yi Allah-Wadai Da Soke Rajistar NDC, Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanar Dimokuraɗiyya

TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

A fadin sanarwar, tun lokacin da suka amshi rahoton, tawagarsu cikin hanzari suka garzaya inda lamarin ya faru tare da daukar yarinyar zuwa babban asibitin Ningi daga bisani aka sauya mata wurin jinya zuwa asibitin kula da masu yoyon fitsari (NOFIC) da ke Ningi, bayan kaurin jikinta aka sake nausawa da ita zuwa asibitin gwamnatin tarayya (FMC) da ke Birnin Kudu a jihar Jigawa domin neman kulawar likitoci.

A cewar Wakil, tun lokacin ‘yansanda suka sha alwashin sai sun cafko wanda ya aikata hakan domin tabbatar da yarinyar ta samua adalcin da ya dace ta samu, “Kan hakan mun cafke wanda ake zargi, Danladi Ibrahim.

“A lokacin da ake tuhumarsa, ya amsa da kansa cewa ya aikata laifin, don haka bincike na cigaba da guduna da zarar aka kammala za mu gurfanar da shi a gaban kuliya.”

Daga bisani rundunar ‘yansandan ta jawo hankalin al’umma da cewa suke sanya ido da lura da yankunansu domin dakile aniyar bata gari a kowani lokaci tare da gaggawar kai rahoton faruwar lamuran da ba daidai ba cikin hanzari domin daukan matakan gaggawa.

Fyade
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

ADC Ta Yi Allah-Wadai Da Soke Rajistar NDC, Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanar Dimokuraɗiyya
Labarai

ADC Ta Yi Allah-Wadai Da Soke Rajistar NDC, Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanar Dimokuraɗiyya

June 27, 2026
TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu
Manyan Labarai

TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

June 27, 2026
Magoya Bayan Pantami Sun Zargi Ana Musgunawa Gombawa Motors A Gombe
Labarai

Magoya Bayan Pantami Sun Zargi Ana Musgunawa Gombawa Motors A Gombe

June 27, 2026
Next Post
Kungiyar Kwadago Za Ta Shiga Yajin Aiki Kan Cire Tallafin Man Fetur

Kungiyar Kwadago Za Ta Shiga Yajin Aiki Kan Cire Tallafin Man Fetur

LABARAI MASU NASABA

Zaben 2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Bayyana Shirinsu Yayin Da INEC Ta Fitar Da Jawalin Zabe

2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Yi Maraba Da Hukuncin Kotu Kan Dakatar Da Jadawalin INEC

June 27, 2026
ADC Ta Yi Allah-Wadai Da Soke Rajistar NDC, Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanar Dimokuraɗiyya

ADC Ta Yi Allah-Wadai Da Soke Rajistar NDC, Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanar Dimokuraɗiyya

June 27, 2026
TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

June 27, 2026
Magoya Bayan Pantami Sun Zargi Ana Musgunawa Gombawa Motors A Gombe

Magoya Bayan Pantami Sun Zargi Ana Musgunawa Gombawa Motors A Gombe

June 27, 2026
Babu Wani Saɓani Tsakanin Osimhen Da Lookman – Ndidi

Babu Wani Saɓani Tsakanin Osimhen Da Lookman – Ndidi

June 27, 2026
Gasar Kofin Duniya: Senegal Ta Kai Zagaye Na 32 Bayan Lallasa Iraki Da Ci 5-0

Gasar Kofin Duniya: Senegal Ta Kai Zagaye Na 32 Bayan Lallasa Iraki Da Ci 5-0

June 27, 2026
Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Sabuwar Dokar Shaidar Ɗan Ƙasa, Duba Abin Da Ta Ƙunsa

Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Sabuwar Dokar Shaidar Ɗan Ƙasa, Duba Abin Da Ta Ƙunsa

June 27, 2026
Fyade

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)

June 27, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

An Kama Uwa Da Abokiyar Burminta Kan Kisan Jariri A Jihar Yobe

June 27, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Wa Manoma 2,930 Buhun Taki 11,720 A Abuja

June 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.