• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sabon Shugaban Kamfanin Jiragen Saman Nijeriya Ya Yi Tonon Silili

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Sabon Shugaban Kamfanin Jiragen Saman Nijeriya Ya Yi Tonon Silili
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Tsawon lokacin da ‘yan Nijeriya suke dakon jiran fara aikin kamfanin jiragen saman Nijeriya da tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya alkawaranta, lamarin ya zama bambara-kwai, yayin da sabon shugaban kamfanin ya yi tonan silili a wannan mako.

Shugaban kafanin jiragen saman Nijeriya, Kaftin Dayo Olumide ya shaida wa kwamitin majalisar dattawa mai kula da hidimar sufurin jiragen sama cewa, jirgin da tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya kaddamar a kwanakin baya da cewa mallakan Nijeriya, zancen ba haka yake ba, domin hayarsu aka dauko daga kasar Habasha (Ethiopia) kwanaki kadan aka sauya masu launi da rubuta sunan ‘Nigeria Air’ da tambarin kasar a jiki domin a yaudari ‘yan Nijeriya da masu ruwa da tsaki.

  • Zuba Ruwan Dagwalon Nukiliya Cikin Teku Da Japan Ke Shirin Yi Zai Illata Duk Fadin Duniya
  • Cire Tallafin Mai: Tinubu Ya Gana Da Manyan Dillalan Fetur, Ya Ba Da Umarnin Kawo Dauki

Ya ce idan Nijeriya za ta tafiyar da ragamar jirgi, dole ne kayan aikinsa su kasance masu rajista da Nijeriya, kuma sai an samu lasisi da izinin gudanarwa da sauran abubuwan da suke akwai. Ya tabbatar wa duniya da cewa jirgin da aka ce mallakin Nijeriya ne aronsa aka dauko na ‘yan kwanaki kuma tunin aka mayar wa masu shi da kayansu.

Yadda Zancen Ya Faro

A ‘yan awanni da ba su zarce 72 da gwamnatin Buhari ta kammala wa’adinta, gwamnatin kasar ta kaddamar da jirgin na Nijeriya a cibiyar zirga-zirgan jiragen sama da ke filin sauka da tashi na Nnamdi Azikiewe da ke Abuja.

A jawabinsa a wajen kaddamarwar, tsohon Ministan sufuri, Hadi Sirika, ya ce da kyakkyawar hadin guiwa tsakanin kamfanin sufurin jiragen kasar Habasha (Ethiopia) da ake son sayar wa Nijeriya babban jirgin, hakan zai kara kyautata alakar kasuwanci a tsakanin kasashen biyu.

“Wannan daya ne daga cikin abubuwan da aka rasa a bangaren sufurin jirage a Nijeriya, jirgin ya yi daidai da matakin kasuwanci da ake da shi a Nijeriya. A zahiri, muna bukatar irin wannan jirgin don haka mun rattaba masa suna ‘Nigeria Air Limited’.”

Ya ce tun shekarar 2016, aka fara yunkurin mallakar jirgin amma sai a wannan karon aka samu cimmawa, “Don haka jirgin zai kasance a nan kuma za mu fara jigila daidai yadda za mu iya yi,” a fadin Sirika.

Mafi yawan al’ummar Nijeriya sun shiga farin ciki da murna da jin an samu jirgin sama mallakin kasar, inda suka yi fatan hakan zai kawo saukin wasu lamuran, sai dai kash.

Ta Ina Gizo Ke Saka: Shugaban Kamfanin Ya Fayyace Zare Da Abawa

Shugaban kamfanin jirgin saman Nijeriya, Kaftin Dayo Olumide, ya shaida cewa, jirgin hadakar da aka kaddamar a Nijeriya bai da rajista. Ya ce an dauko jirgin ne daga kasar Habasha (Ethiopia) a matsayin wanda zai yi ‘yan kwanaki kuma da an kammala abun da ake son yi da shi aka dauka a mayar can.

Ya kara da cewa Nijeriya tana da lasisi din mallakar filayen jirgin sama ne kawai daya daga cikin izini guda biyu da ake bukata kafin gudanar da harkokin sufuri. Ya ce kasar ba ta da izinin fara gudanar da harkokin kasuwanci da jiragen, balle har ya zo a ce ta samu jirginta da za ta fara gudanar da harkokin kasuwanci da shi.

Ya kara da cewa, “Zan fara ba ka amsar tambayarka kafin na ci gaba. Jirgin da aka kawo ya kuma koma inda ya fito, domin hayarsa aka dauko.

“Dukkanmu a nan idan muna da bikin aure a Senegal, za mu iya daukar hanyar jirgi. Ba ka da bukatar sai ka nemi izinin yin hakan, kawai hayar jirgin za ka yi, kuma jirgin za ka biya kudinsa ne, zai zo nan take kuma har ka kwashi fasinjarka ka yi tafiyarka.

“Wannan shi ne abun da muka yi. Amma a kan wannan lamarin aka kaddamar. Tun 2018, duk abun da kuka gani da sunan jirgin mallakin Nijeriya kawai a hoto ne, zane ne ba jirgi ne na hakika ba, amma ina tunanin lokaci ya yi da za mu fara nuna yadda jirgin gaske zai kasance. Kuna gani muna da masu zuba hannun jari, za su iya zuba kudinsu na tsawon shekara 10 zuwa 15. Don haka suna da bukatar a nuna musu hakikanin yadda ake son jirgin ya kasance.

“Don haka mun kawo don mu nuna musu jirgin da yadda ake son ya kasance. Daga nan kuma sai yanayin social media ya shigo ciki.

“Wannan jirgin da ake magana a kai na da rajista ne da Ethiopia. Me ya sa zai kasance mai rajista da Ethiopia? Idan Nijeriya za ta tafiyar da ragamar jirginta, dole ne ya kasance jirgin na dauke da rajistan Nijeriya na ranar 5 ga Nuwamba. Amma jirgin baya dauke da rajistan 5 ga watan Nuwamba saboda hayarsa aka dauko na ‘yan kwanaki kuma da ya kammala ya koma abunsa.

“Idan muka son mu samun lasisin wanda aiki na ne, dole ne mu yi wasu abubuwan, daga ciki dole ne ya zama muna da jirage akalla uku kafin NCA ta ba mu lasisi, sannan dukkanin wadannan jiragen dole ne su kasance masu rajistan Nijeriya.

“Akwai matakai guda biyar da mutum zai bi kafin ya samu lasisi. Mun doshi mataki na daya da na biyu, amma matsalar da muke fuskanta shi ne, idan ka canza abun da muke kira ‘post holders’, wani bangaren kwararru ne da ke hada daraktan kulawa, babban matukin jirgi, idan ka canza su da wasu gaba daya, to ka sake komawa baya kan shirinka, sai an sake musu tambayoyi domin cika ka’idojin hukumar. Ko da yake, sake komawa bayan ba yana nunin ka yi wani abu na kuskure ba ne, hakan gyara ne a tsarin da ake bi.

“Don haka, lokacin da aka kawo wannan jirgin a matsayin na haya, kawai sai kowa da kowa ya kama cewa mun kaddamar da jirgin Nijeriya.”

‘Yan Majalisa Sun Nuna Damuwarsu

A bangarensu, shugaban kwamitin na majalisar dattawan, Sanata Biodun Olujimi  da Sanata Smart Adeyemi sun ce, wannan abun takaici ne yadda kokonto da wasiwasi ya shiga cikin lamarin aikin samar da jirgin Nijeriya.

Kazalika, a yayin zaman, ‘yan majalisan sun yi tir da matakan da aka bi, sun misalta hakan a matsayin damfara da zamba.

Nnolim Nnaji ya nuna damuwar bayan da manyan masu ruwa da tsaki a Nijeriya da kamfanin jiragen Ethiopian suka nuna cewa ba su da masaniya kan kaddamar da jirgin da aka ce an yi a Nijeriya kwanakin baya.

Ma’aikatar sufuri ta yi ikirarin cewa Nijeriya ta nuna jirgin ne kawai amma ba kaddamarwa ba.

Mambobin kwamitin majalisar sun nuna bacin ransu da damuwarsu ne lokacin da hukumar kula da sararin samanin Nijeriya (NAMA) ta ce jirgin da aka makala masa launin Nijeriya hayarsa aka yi zuwa Nijeriya.

Wasu da suka kaddamar da maganar NAMA din, sun ce ana iya sauya launin jirgin da Nijeriya ta dauko hayarsa zuwa kowani irin launi da ake so.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Jiragen SamaNigeria AirNijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugabar Kasar Honduras Ta Fara Ziyara a Kasar Sin

Next Post

Motocin Fasinja Kirar Sin Da Aka Sayar Sun Karu Da Kashi 37.6 A Mayu

Related

Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25
Labarai

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

5 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

5 hours ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)
Labarai

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

6 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

7 hours ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

9 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

10 hours ago
Next Post
Motocin Fasinja Kirar Sin Da Aka Sayar Sun Karu Da Kashi 37.6 A Mayu

Motocin Fasinja Kirar Sin Da Aka Sayar Sun Karu Da Kashi 37.6 A Mayu

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.