ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sabon Shugaban Kamfanin Jiragen Saman Nijeriya Ya Yi Tonon Silili

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Tsawon lokacin da ‘yan Nijeriya suke dakon jiran fara aikin kamfanin jiragen saman Nijeriya da tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya alkawaranta, lamarin ya zama bambara-kwai, yayin da sabon shugaban kamfanin ya yi tonan silili a wannan mako.

Shugaban kafanin jiragen saman Nijeriya, Kaftin Dayo Olumide ya shaida wa kwamitin majalisar dattawa mai kula da hidimar sufurin jiragen sama cewa, jirgin da tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya kaddamar a kwanakin baya da cewa mallakan Nijeriya, zancen ba haka yake ba, domin hayarsu aka dauko daga kasar Habasha (Ethiopia) kwanaki kadan aka sauya masu launi da rubuta sunan ‘Nigeria Air’ da tambarin kasar a jiki domin a yaudari ‘yan Nijeriya da masu ruwa da tsaki.

  • Zuba Ruwan Dagwalon Nukiliya Cikin Teku Da Japan Ke Shirin Yi Zai Illata Duk Fadin Duniya
  • Cire Tallafin Mai: Tinubu Ya Gana Da Manyan Dillalan Fetur, Ya Ba Da Umarnin Kawo Dauki

Ya ce idan Nijeriya za ta tafiyar da ragamar jirgi, dole ne kayan aikinsa su kasance masu rajista da Nijeriya, kuma sai an samu lasisi da izinin gudanarwa da sauran abubuwan da suke akwai. Ya tabbatar wa duniya da cewa jirgin da aka ce mallakin Nijeriya ne aronsa aka dauko na ‘yan kwanaki kuma tunin aka mayar wa masu shi da kayansu.

Yadda Zancen Ya Faro

A ‘yan awanni da ba su zarce 72 da gwamnatin Buhari ta kammala wa’adinta, gwamnatin kasar ta kaddamar da jirgin na Nijeriya a cibiyar zirga-zirgan jiragen sama da ke filin sauka da tashi na Nnamdi Azikiewe da ke Abuja.

A jawabinsa a wajen kaddamarwar, tsohon Ministan sufuri, Hadi Sirika, ya ce da kyakkyawar hadin guiwa tsakanin kamfanin sufurin jiragen kasar Habasha (Ethiopia) da ake son sayar wa Nijeriya babban jirgin, hakan zai kara kyautata alakar kasuwanci a tsakanin kasashen biyu.

“Wannan daya ne daga cikin abubuwan da aka rasa a bangaren sufurin jirage a Nijeriya, jirgin ya yi daidai da matakin kasuwanci da ake da shi a Nijeriya. A zahiri, muna bukatar irin wannan jirgin don haka mun rattaba masa suna ‘Nigeria Air Limited’.”

Ya ce tun shekarar 2016, aka fara yunkurin mallakar jirgin amma sai a wannan karon aka samu cimmawa, “Don haka jirgin zai kasance a nan kuma za mu fara jigila daidai yadda za mu iya yi,” a fadin Sirika.

Mafi yawan al’ummar Nijeriya sun shiga farin ciki da murna da jin an samu jirgin sama mallakin kasar, inda suka yi fatan hakan zai kawo saukin wasu lamuran, sai dai kash.

Ta Ina Gizo Ke Saka: Shugaban Kamfanin Ya Fayyace Zare Da Abawa

Shugaban kamfanin jirgin saman Nijeriya, Kaftin Dayo Olumide, ya shaida cewa, jirgin hadakar da aka kaddamar a Nijeriya bai da rajista. Ya ce an dauko jirgin ne daga kasar Habasha (Ethiopia) a matsayin wanda zai yi ‘yan kwanaki kuma da an kammala abun da ake son yi da shi aka dauka a mayar can.

Ya kara da cewa Nijeriya tana da lasisi din mallakar filayen jirgin sama ne kawai daya daga cikin izini guda biyu da ake bukata kafin gudanar da harkokin sufuri. Ya ce kasar ba ta da izinin fara gudanar da harkokin kasuwanci da jiragen, balle har ya zo a ce ta samu jirginta da za ta fara gudanar da harkokin kasuwanci da shi.

Ya kara da cewa, “Zan fara ba ka amsar tambayarka kafin na ci gaba. Jirgin da aka kawo ya kuma koma inda ya fito, domin hayarsa aka dauko.

“Dukkanmu a nan idan muna da bikin aure a Senegal, za mu iya daukar hanyar jirgi. Ba ka da bukatar sai ka nemi izinin yin hakan, kawai hayar jirgin za ka yi, kuma jirgin za ka biya kudinsa ne, zai zo nan take kuma har ka kwashi fasinjarka ka yi tafiyarka.

“Wannan shi ne abun da muka yi. Amma a kan wannan lamarin aka kaddamar. Tun 2018, duk abun da kuka gani da sunan jirgin mallakin Nijeriya kawai a hoto ne, zane ne ba jirgi ne na hakika ba, amma ina tunanin lokaci ya yi da za mu fara nuna yadda jirgin gaske zai kasance. Kuna gani muna da masu zuba hannun jari, za su iya zuba kudinsu na tsawon shekara 10 zuwa 15. Don haka suna da bukatar a nuna musu hakikanin yadda ake son jirgin ya kasance.

“Don haka mun kawo don mu nuna musu jirgin da yadda ake son ya kasance. Daga nan kuma sai yanayin social media ya shigo ciki.

“Wannan jirgin da ake magana a kai na da rajista ne da Ethiopia. Me ya sa zai kasance mai rajista da Ethiopia? Idan Nijeriya za ta tafiyar da ragamar jirginta, dole ne ya kasance jirgin na dauke da rajistan Nijeriya na ranar 5 ga Nuwamba. Amma jirgin baya dauke da rajistan 5 ga watan Nuwamba saboda hayarsa aka dauko na ‘yan kwanaki kuma da ya kammala ya koma abunsa.

“Idan muka son mu samun lasisin wanda aiki na ne, dole ne mu yi wasu abubuwan, daga ciki dole ne ya zama muna da jirage akalla uku kafin NCA ta ba mu lasisi, sannan dukkanin wadannan jiragen dole ne su kasance masu rajistan Nijeriya.

“Akwai matakai guda biyar da mutum zai bi kafin ya samu lasisi. Mun doshi mataki na daya da na biyu, amma matsalar da muke fuskanta shi ne, idan ka canza abun da muke kira ‘post holders’, wani bangaren kwararru ne da ke hada daraktan kulawa, babban matukin jirgi, idan ka canza su da wasu gaba daya, to ka sake komawa baya kan shirinka, sai an sake musu tambayoyi domin cika ka’idojin hukumar. Ko da yake, sake komawa bayan ba yana nunin ka yi wani abu na kuskure ba ne, hakan gyara ne a tsarin da ake bi.

“Don haka, lokacin da aka kawo wannan jirgin a matsayin na haya, kawai sai kowa da kowa ya kama cewa mun kaddamar da jirgin Nijeriya.”

‘Yan Majalisa Sun Nuna Damuwarsu

A bangarensu, shugaban kwamitin na majalisar dattawan, Sanata Biodun Olujimi  da Sanata Smart Adeyemi sun ce, wannan abun takaici ne yadda kokonto da wasiwasi ya shiga cikin lamarin aikin samar da jirgin Nijeriya.

Kazalika, a yayin zaman, ‘yan majalisan sun yi tir da matakan da aka bi, sun misalta hakan a matsayin damfara da zamba.

Nnolim Nnaji ya nuna damuwar bayan da manyan masu ruwa da tsaki a Nijeriya da kamfanin jiragen Ethiopian suka nuna cewa ba su da masaniya kan kaddamar da jirgin da aka ce an yi a Nijeriya kwanakin baya.

Ma’aikatar sufuri ta yi ikirarin cewa Nijeriya ta nuna jirgin ne kawai amma ba kaddamarwa ba.

Mambobin kwamitin majalisar sun nuna bacin ransu da damuwarsu ne lokacin da hukumar kula da sararin samanin Nijeriya (NAMA) ta ce jirgin da aka makala masa launin Nijeriya hayarsa aka yi zuwa Nijeriya.

Wasu da suka kaddamar da maganar NAMA din, sun ce ana iya sauya launin jirgin da Nijeriya ta dauko hayarsa zuwa kowani irin launi da ake so.

Nijeriya
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
Motocin Fasinja Kirar Sin Da Aka Sayar Sun Karu Da Kashi 37.6 A Mayu

Motocin Fasinja Kirar Sin Da Aka Sayar Sun Karu Da Kashi 37.6 A Mayu

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.