ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zuba Ruwan Dagwalon Nukiliya Cikin Teku Da Japan Ke Shirin Yi Zai Illata Duk Fadin Duniya

by CMG Hausa
3 years ago
Nukiliya

Gobe ranar teku ce ta kasa da kasa karo na 15, babban taron MDD karo na 63 ya tsai da ranar 8 ga watan Yunin kowace shekara ranar teku ta kasa da kasa, don jan hankalin duniya muhimmancin kiyaye teku, wanda ke da babbar ma’ana ga bunkasuwar al’umma.

Amma a abin takaici ne, albarkacin wannan muhimmiyar rana, kasar Japan har yanzu tana kare aniyarta ta zuba ruwan dagwalon nukiliya ta tashar nukiliya ta Fukushima cikin teku bisa son kanta. Kwanan nan, kafar NHK ta kasar Japan ta ba da labarin cewa, an riga an fara zuba ruwan teku cikin bututun da ruwan dagwalon nukiliya zai bi a Fukushima.

  • An Bude Taron Kasa Da Kasa Na Baje Kolin Harkokin Al’adu A Shenzhen

Shirin nan na Japan ya jawo suka daga gida da ma waje, sai dai gwamnatin Japan ta yi ta neman wanke kanta ta kowa ce hanya.

ADVERTISEMENT

Gwamnatin Japan ta ce ruwan dagwalon ba zai kawo illa ga muhallin teku ba, amma ko hakan gaskiya ne? A hakika, ruwan dagwalon tashar Fukushima na kunshe da sinadaran nukiliya masu guba sama da 60. Kamfanin samar da wutar lantarki na Tokyo ya ba da wani rahoto a ran 5 ga wata cewa, an gano abin tiriri na Cesium a jikin nau’in kifin da aka kama a gulf din tashar nukiliya ta Fukushima, yawansa ya ninka sau 180 bisa na ma’aunin da aka tanada.

A sa’i daya kuma, igiyar ruwa a wannan wuri na da karfi matuka, matakin da ya sa idan an zuba ruwan dagwalon nukiliya cikin teku, zai yadu zuwa duk fadin tekun duniya a cikin shekaru 10 masu zuwa, abin da zai kawo babbar illa ga muhallin teku da lafiyar jikin Bil Adama.

LABARAI MASU NASABA

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Bisa dokar kasa da kasa, ruwan dagwalon nukiliya na Fukushima shara ce, dole ne a ajiye su a maimakon zuba su a cikin teku. Misali a tashar samar da wutar lantarki ta amfani da karfin nukiliya ta kasar Faransa, an kafa cibiyar adana sharar da tashar ke samarwa, matakin da ya fi dacewa.

Gwamnatin Japan ta fitar da shirye-shirye da dama game da yadda za a yi da ruwan dagwalon nukiliya na tashar Fukushima tun daga shekarar 2013, amma daga karshe ta zabi wannan shiri maras imani don yin tsimin kudi da kare kanta.

Shin ko gwamnatin Japan ba ta da isashen kudi? A’a, ba ta da imani ne! Matakin ta zai kawowa muhalli matukar barazana, har ma ya illata makomar Bil Adama baki daya. (Mai zana da rubuta: MINA)

Nukiliya
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
Daga Birnin Sin

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”
Daga Birnin Sin

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines
Daga Birnin Sin

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Next Post
Hajjin Bana: Ku Zama Jakadu Na Kwarai – Gwamnan Gombe Ga Maniyyata

Hajjin Bana: Ku Zama Jakadu Na Kwarai - Gwamnan Gombe Ga Maniyyata

LABARAI MASU NASABA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

June 13, 2026
Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

June 13, 2026
Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

June 13, 2026
Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.