• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zambar Kudi: Kotu Ta Tasa Keyar Dillalin Gidaje Zuwa Gidan Kaso

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Zamba

Wanda ake tuhumar na fuskantar tuhume-tuhume uku da suka hada da hadin baki da shi, domin yaudara wurin cin kudin, wanda sashen yaki da masu damfarar na ‘yansanda na musamman yake tuhumarsa da shi.

An gurfanar da Nwogu ne tare da kamfaninsa, Libelihood Homes Limited, da sauran wadanda ake tsare da su a gaban mai shari’a Peter Lifu.

  • Zuba Ruwan Dagwalon Nukiliya Cikin Teku Da Japan Ke Shirin Yi Zai Illata Duk Fadin Duniya
  • Kotu Ta Bukaci Masu Kalubalantar Nasarar Tinubu Su Biya Miliyan 10 Kowannensu

Dansanda mai shigar da kara, Emmanuel Jackson, ya shaida wa kotun cewa wanda ake tuhuma da sauran abokansa yanzu, sun aikata laifin ne a cikin wannan shekarar.

Jackson ya shaida wa kotun cewa sun damfari cocin naira miliyan 65 daga wani coci da ke unguwar Ojodu a Jihar Legas ta hanyar yi mata karyar kamfaninsa na da filayen sayarwa a Karamar Hukumar Ewekoro Jihar Ogun da Agbara babban titin a Legas tare da yin karyar cewa suna da filayen sayarwa a Karamar Hukumar Ewekoro. Jihar Ogun, da Agbara, Badagry Edpressway a Legas, ya ce shi da jama’arsa ne suka karbi kudin.

Ya ce bayan karbar kudin daga cocin, wanda ake kara ya kasa bayar da filin kamar yadda ya yi alkawari, sannan kuma ya kasa biyan cocin kudin.

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

A cewarsa, laifukan sun ci karo da sashe na 8 (a), 1 (1) (8) da kuma hukunci a karkashin sashe na 1 (3) na kudin zamba da sauran laifuka masu alaka da zamba, mai lamba 14 na 2006 da sashe na 15(2) (b) na Dokar Hana Cin Kudin Zamba na shekarar 2011 kamar yadda aka gyara a 2012.

Amma kuma abin mamaki Nwogu ya musanta zargin da ake masa.

Bayan da ya shigar da kara, dansandan ya bukaci kotun da ta ci gaba da sauraren karar, sannan kuma ya bukaci kotun da ta ci gaba da tsare wanda ake kara a gidan yari na Nijeriya har sai an kammala tantance zargin da ake yi masa.

Sai dai lauyan wanda ake tuhuma, Bernard Omang, ya nemi kotun da ta amince da wanda yake karewa da bayar da belinsa cikin sharudan sassauci.

Kotu ta yi watsi da bukatar tasa bisa hujjar cewa babu wata bukata da ta dace da za ta goyi bayan bukatarsa.

Don haka mai shari’a Lifu ya bayar da umarnin a tsare wanda ake tuhuma a gidan yari na Ikoyi sannan ya dage ci gaba da shari’ar har zuwa ranar 14 ga watan Yuni.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi
Kotu Da Ɗansanda

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

October 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

October 4, 2025
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Farmaki Masu Safarar Muggan Kwayoyi A Sassan Nijeriya

September 27, 2025
Next Post
Wani Mutum Ya Kashe Kishiyar Mahaifiyarsa A Kogi

An Ceto Mata Masu Ciki 21 A Cibiyar Cinikin Jarirai A Abiya

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura

November 7, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki

Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki

November 7, 2025
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

November 7, 2025
Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

November 7, 2025
Yadda Duniya Ta Fara Wayewa Tun Daga Zamanin Annabi Nuhu (AS) Har Manzon Allah (SAW) Ya Zo Ya Cika Komai (2)

Yadda Duniya Ta Fara Wayewa Tun Daga Zamanin Annabi Nuhu (AS) Har Manzon Allah (SAW) Ya Zo Ya Cika Komai (2)

November 7, 2025
Yaduwar Juyin Mulki A Afirka

Yaduwar Juyin Mulki A Afirka

November 7, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Hanyoyin Noma Na Gargajiya Ba Za Su Iya Wadata Abinci A Nijeriya Ba -Masanin Kimiyya

November 7, 2025
An Kaddamar Da Taron Kolin Wuzhen Na Ayyuka Masu Nasaba Da Yanar Gizo

An Kaddamar Da Taron Kolin Wuzhen Na Ayyuka Masu Nasaba Da Yanar Gizo

November 7, 2025
Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah

November 7, 2025
Sin Ta Kadammar Da Babban Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Yaki Na CNS Fujian a Rundunar Sojan Ruwanta

Sin Ta Kadammar Da Babban Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Yaki Na CNS Fujian a Rundunar Sojan Ruwanta

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.