• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zambar Kudi: Kotu Ta Tasa Keyar Dillalin Gidaje Zuwa Gidan Kaso

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Zambar Kudi: Kotu Ta Tasa Keyar Dillalin Gidaje Zuwa Gidan Kaso
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wanda ake tuhumar na fuskantar tuhume-tuhume uku da suka hada da hadin baki da shi, domin yaudara wurin cin kudin, wanda sashen yaki da masu damfarar na ‘yansanda na musamman yake tuhumarsa da shi.

An gurfanar da Nwogu ne tare da kamfaninsa, Libelihood Homes Limited, da sauran wadanda ake tsare da su a gaban mai shari’a Peter Lifu.

  • Zuba Ruwan Dagwalon Nukiliya Cikin Teku Da Japan Ke Shirin Yi Zai Illata Duk Fadin Duniya
  • Kotu Ta Bukaci Masu Kalubalantar Nasarar Tinubu Su Biya Miliyan 10 Kowannensu

Dansanda mai shigar da kara, Emmanuel Jackson, ya shaida wa kotun cewa wanda ake tuhuma da sauran abokansa yanzu, sun aikata laifin ne a cikin wannan shekarar.

Jackson ya shaida wa kotun cewa sun damfari cocin naira miliyan 65 daga wani coci da ke unguwar Ojodu a Jihar Legas ta hanyar yi mata karyar kamfaninsa na da filayen sayarwa a Karamar Hukumar Ewekoro Jihar Ogun da Agbara babban titin a Legas tare da yin karyar cewa suna da filayen sayarwa a Karamar Hukumar Ewekoro. Jihar Ogun, da Agbara, Badagry Edpressway a Legas, ya ce shi da jama’arsa ne suka karbi kudin.

Ya ce bayan karbar kudin daga cocin, wanda ake kara ya kasa bayar da filin kamar yadda ya yi alkawari, sannan kuma ya kasa biyan cocin kudin.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

A cewarsa, laifukan sun ci karo da sashe na 8 (a), 1 (1) (8) da kuma hukunci a karkashin sashe na 1 (3) na kudin zamba da sauran laifuka masu alaka da zamba, mai lamba 14 na 2006 da sashe na 15(2) (b) na Dokar Hana Cin Kudin Zamba na shekarar 2011 kamar yadda aka gyara a 2012.

Amma kuma abin mamaki Nwogu ya musanta zargin da ake masa.

Bayan da ya shigar da kara, dansandan ya bukaci kotun da ta ci gaba da sauraren karar, sannan kuma ya bukaci kotun da ta ci gaba da tsare wanda ake kara a gidan yari na Nijeriya har sai an kammala tantance zargin da ake yi masa.

Sai dai lauyan wanda ake tuhuma, Bernard Omang, ya nemi kotun da ta amince da wanda yake karewa da bayar da belinsa cikin sharudan sassauci.

Kotu ta yi watsi da bukatar tasa bisa hujjar cewa babu wata bukata da ta dace da za ta goyi bayan bukatarsa.

Don haka mai shari’a Lifu ya bayar da umarnin a tsare wanda ake tuhuma a gidan yari na Ikoyi sannan ya dage ci gaba da shari’ar har zuwa ranar 14 ga watan Yuni.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: EFCCKotu Da Dan SandaZamba
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ba Amurka Ce Ta Yanke Shawarar Kasancewar Sin Kasa Mai Tasowa Ba

Next Post

An Ceto Mata Masu Ciki 21 A Cibiyar Cinikin Jarirai A Abiya

Related

‘Yan Sanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Jefe Wani Direba Har Lahira A Ondo
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

1 week ago
Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe
Kotu Da Ɗansanda

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

1 week ago
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

2 months ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum 245 Da Miyagun Kwayoyi Da Makamai A Abuja

3 months ago
‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda

3 months ago
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Na Farautar Wadanda Suka Kashe Dalibi A Katsina

3 months ago
Next Post
Wani Mutum Ya Kashe Kishiyar Mahaifiyarsa A Kogi

An Ceto Mata Masu Ciki 21 A Cibiyar Cinikin Jarirai A Abiya

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.