• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Ceto Mata Masu Ciki 21 A Cibiyar Cinikin Jarirai A Abiya

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Wani Mutum Ya Kashe Kishiyar Mahaifiyarsa A Kogi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar Sojin Nijeriya ta 14, Ohafia, ta kai samame a wata masana’antar jarirai da ke Umunkpei Nbosi a Karamar Hukumar Isiala-Ngwa a Jihar Abia, wanda ake zargin wani Dan yankin ne ke sarrafa ta.

Dakarun sun isa wurin ne inda suka ceto mata 22 daga cikinsu 21 na dauke da juna biyu ciki har da jarirai 2 (maza da mace data).

  • Gwamnatin Abba Kabir Za Ta Inganta Tsarin Makarantun Tsangayu A Kano – Falaki
  • Yanzu-Yanzu Tinubu Na Ganawa Da Kwakwaso

Sauran kayayyakin da aka samu a wurin sun hada da janareta Tiger, wayoyin wuta, tukunyar gas, buhun shinkafa, tumatur kwali guda, man kayana marmari 4, buhunan garri 5, da kuma kayan miya leda 2.

Sojoji sun kai samame a masana’antar jarirai ne biyo bayan rahoton sirri da aka samu cewa mai kamfanin na sayar da wasu jariran ga ‘yan fashi da makami domin yin tsafi da su, wasu kuma domin safarar yara.

An yi zargin cewa wata ma mata tana da take zaune a yankin tana mu’amala da su kuma a wasu lokutan, ana ganin sassan jikin mutane a kusa da ginin gidanta.

Labarai Masu Nasaba

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

‘Yansanda Sun Kama Mutum 245 Da Miyagun Kwayoyi Da Makamai A Abuja

A cewar wani mamban rundunar, mai kamfanin jariran a halin yanzu yana nan a hannun rundunar ana ci gaba da kamo sauran domin gudanar da bincike.

Sai dai rundunar sojin ta kama wata mata mai suna Katherine Oyechi Ngwanma, mai shekaru 34, mai dafa abinci a wurin.

Matan masu juna biyu, da jariran, an mika su ga gwamnatin Jihar Abia domin ci gaba da kula da su.

Ba a iya samun sabon jami’in hulda da jama’a na ‘yansanda a jihar, Chinaka Maureen, domin jin ta bakinsa ba.

Sojojin sun samu jagorancin jami’in hulda da jama’a na rundunar soji, Brigade Ohafia 14, Laftanar Omale Innocent Prince, da mai bai wa gwamna shawara kan harkokin yada labarai Aled Otti, Mista Ferdinand Ekeoma.

A wata hira da aka yi da shi bayan aikin, Ekeoma ya yaba wa rundunar sojin bisa aikin, inda ya bayyana cewa babu hujjar dalilin da ya sa “irin wannan abu ya kamata ya faru a kowane yanki na Jihar Abia”.

Ya ba da tabbacin cewa gwamnatin Aled Otti za ta tsaftace jihar, yayin da gwamnati tare da hadin gwiwar hukumomin tsaro za su gudanar da cikakken bincike kan lamarin.

Gwamnatin Otti, in ji shi, ba za ta bari irin wannan lamari ya ci gaba ba a kowane bangare na jihar ba daga yanzu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbiyaJarirai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zambar Kudi: Kotu Ta Tasa Keyar Dillalin Gidaje Zuwa Gidan Kaso

Next Post

NDLEA Ta Kwace Kilo Giram 390 Na Muggan Kwayoyi

Related

Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

4 weeks ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum 245 Da Miyagun Kwayoyi Da Makamai A Abuja

2 months ago
‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda

2 months ago
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Na Farautar Wadanda Suka Kashe Dalibi A Katsina

2 months ago
Rikita-rikitar Da Ta Biyo Bayan Mutuwar Mawaki Mohbad
Kotu Da Ɗansanda

MohBad: Nurse Za Ta Fuskanci Shari’a, Sannan Kotu Ta Wanke Naira Marley, Sam Larry Da PrimeBoy

2 months ago
‘Yansanda Sun Kubutar Da Wata Mata Da Aka Yi Garkuwa Da Ita A Otal Din Abuja
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kubutar Da Wata Mata Da Aka Yi Garkuwa Da Ita A Otal Din Abuja

3 months ago
Next Post
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance

NDLEA Ta Kwace Kilo Giram 390 Na Muggan Kwayoyi

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.