• English
  • Business News
Friday, October 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zan Yi Aiki A Bayyane Tare Da Shugabannin Majalisa Ta 10 – Tinubu

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Tinubu

Shugaban kasa Bola Tinubu ya yaba da zaben Godswill Akpabio da Tajudeen Abbas a matsayin shugaban majalisar dattawa da shugaban majalisar wakilai, inda ya tabbatar da cewa zai yi aiki a fili tare da sabbin shugabannin majalisar.

Ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ya sanya wa hannu da kansa a ranar Talata, inda ya bayyana nasarar shugabannin majalisar guda biyu da mataimakansu, Jibril Barau da Benjamin Kalu a matsayin babban ci gaban da aka samu a cikin dimokuradiyyar Nijeriya.

  • An Cafke Mai Sojan Gona A Matsayin Jami’in EFCC Da Sojoji
  • ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Daliban Jami’ar Jos 7

Tinubu ya ce, “A matsayina na shugabanku a shirye nake in yi aiki tare da majalisar dokoki ta kasa a bayyane. ‘Yan Nijeriya na sa ran manyan sanatoci da ‘yan majalisar wakilai za su kafa dokoki da gudanar da ayyukan sa ido da za su inganta ayyukan gwamnati don samun sakamako mai kyau ciki har da inganta rayuwarsu.

“A yayin aikinmu tare, ana iya samun rashin jituwa. Idan ba mu yarda da haka ba, to za mu yaudari kanmu, rashin son zuciya da neman rage wa majalisar dokoki ta kasa ko wani mamba ba zai taba haifar mana da da mai ido ba.”

Shugaban ya tunatar da su cewa, zaben da takwarorinsu suka yi masu a matsayin shugabanni da kuma dora ragamar shugabancin majalisar babban abin alfahari ne da ke tattare da gagarumin nauyi tare da fatan za su ba da marasa kunya wajen aiki kafada da kafada da sauran ‘yan majalisa da kuma daukacin ‘yan Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

Ya jajanta wa Abdulaziz Yari da Idris Wase da kuma Aminu Jaji wadanda suka fadi zabe bisa inganta tsarin shugabanni majalisa ta 10. Ya yi kira gare su da su ci gaba da gajircewa kamar yadda suka yi a takarar shugabancin majalisar dokokin kasa wajen gudanar da ayyukansu ga al’ummar mazabarsu da kuma  Nijeriya.

Tinubu ya taya daukacin ‘yan majalisar dokoki ta kasa wadanda a suka shiga aikin yi wa al’ummar kasar nan hidima.

Ya gargade su da cewa, “Muna yin kira ga dukkaninmu mu yi kokarin sauke nauyin da ke kanmu da kuma amfani da rantsuwar da muka yi na hakkin hidimta wa kasarmu. Lokaci ya yi da za mu ci gaba da tafiya tare wajen gudanar da harkokin mulki domin ci gaban Nijeriya.

 “Mutane a fadin kasar nan suna sa rai sosai daga gare mu. Suna son mu sauke nauyinsu na tattalin arziki. Suna son mu kawar da rashin tsaro domin manomanmu na karkara su je gonakinsu su noma abincin da muke ci.”

“Mutanenmu sun zuba mana ido mu gyara arzikin kasarmu da kuma kawar da duk wani shingen da ke hana ci gaba. Duk wadannan za mu iya yi ne kadai idan muka jajirce. Za mu iya cimma dukkan kyawawan abubuwan da muka alkawarta a lokacin yakin neman zabe idan muka yi aiki tare cikin jituwa da mutunta hakkinmu da kuma maslahar kasarmu.

“Ba za mu yi watsi da wannan damar ba saboda ‘yan Nijeriya suna son mu yi amfani da kowace rana a cikin shekaru hudu masu zuwa. A bisa lamarin gaskiya, mutanenmu suna son mu rubayya kokarin gwamnatinmu. Hakika sun cancanci shugabanci nagari mai cike da adalci wanda zai inganta rayuwarsu. Dole ne mu ba su iya abin da zamu iya.

“Zan ci gaba da abokin kowa don samun zaman lafiya da kwanciyar hankali da ci gaban Nijeriya. Ina kira ga shugabannin majalisar dokoki ta kasa ta 10 da dukkan ‘yan majalisa su yi aiki tare da ni a wannan tafiya ta gwamnati.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
Next Post
Idan Ruwan Dagwalon Nukiliya Bai Gurbata Ba, Me Yasa Japan Ba Ta Ajiye Shi Ba?

Idan Ruwan Dagwalon Nukiliya Bai Gurbata Ba, Me Yasa Japan Ba Ta Ajiye Shi Ba?

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Talauci Da Rashin Tsawon Rai Da ‘Yan Nijeriya Ke Fuskanta

Matsalar Talauci Da Rashin Tsawon Rai Da ‘Yan Nijeriya Ke Fuskanta

October 31, 2025
Matsalar Tsaro: Ko Sabbin Shugabannin Rundunar Soji Za Su Kawo Sauyi?

Matsalar Tsaro: Ko Sabbin Shugabannin Rundunar Soji Za Su Kawo Sauyi?

October 31, 2025
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo

October 30, 2025
An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara

An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara

October 30, 2025
Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 

Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 

October 30, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutum Ɗaya, Sun Kama Mace Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Dajin Kwara 

October 30, 2025
Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC

Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC

October 30, 2025
Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray

Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray

October 30, 2025
Kasar Sin Ce Ke Da Sama Da Rabin Muhimman Makaloli Na Duniya

Kasar Sin Ce Ke Da Sama Da Rabin Muhimman Makaloli Na Duniya

October 30, 2025
Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai

Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai

October 30, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.