ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zan Yi Aiki A Bayyane Tare Da Shugabannin Majalisa Ta 10 – Tinubu

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Tinubu

Shugaban kasa Bola Tinubu ya yaba da zaben Godswill Akpabio da Tajudeen Abbas a matsayin shugaban majalisar dattawa da shugaban majalisar wakilai, inda ya tabbatar da cewa zai yi aiki a fili tare da sabbin shugabannin majalisar.

Ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ya sanya wa hannu da kansa a ranar Talata, inda ya bayyana nasarar shugabannin majalisar guda biyu da mataimakansu, Jibril Barau da Benjamin Kalu a matsayin babban ci gaban da aka samu a cikin dimokuradiyyar Nijeriya.

  • An Cafke Mai Sojan Gona A Matsayin Jami’in EFCC Da Sojoji
  • ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Daliban Jami’ar Jos 7

Tinubu ya ce, “A matsayina na shugabanku a shirye nake in yi aiki tare da majalisar dokoki ta kasa a bayyane. ‘Yan Nijeriya na sa ran manyan sanatoci da ‘yan majalisar wakilai za su kafa dokoki da gudanar da ayyukan sa ido da za su inganta ayyukan gwamnati don samun sakamako mai kyau ciki har da inganta rayuwarsu.

ADVERTISEMENT

“A yayin aikinmu tare, ana iya samun rashin jituwa. Idan ba mu yarda da haka ba, to za mu yaudari kanmu, rashin son zuciya da neman rage wa majalisar dokoki ta kasa ko wani mamba ba zai taba haifar mana da da mai ido ba.”

Shugaban ya tunatar da su cewa, zaben da takwarorinsu suka yi masu a matsayin shugabanni da kuma dora ragamar shugabancin majalisar babban abin alfahari ne da ke tattare da gagarumin nauyi tare da fatan za su ba da marasa kunya wajen aiki kafada da kafada da sauran ‘yan majalisa da kuma daukacin ‘yan Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

Ya jajanta wa Abdulaziz Yari da Idris Wase da kuma Aminu Jaji wadanda suka fadi zabe bisa inganta tsarin shugabanni majalisa ta 10. Ya yi kira gare su da su ci gaba da gajircewa kamar yadda suka yi a takarar shugabancin majalisar dokokin kasa wajen gudanar da ayyukansu ga al’ummar mazabarsu da kuma  Nijeriya.

Tinubu ya taya daukacin ‘yan majalisar dokoki ta kasa wadanda a suka shiga aikin yi wa al’ummar kasar nan hidima.

Ya gargade su da cewa, “Muna yin kira ga dukkaninmu mu yi kokarin sauke nauyin da ke kanmu da kuma amfani da rantsuwar da muka yi na hakkin hidimta wa kasarmu. Lokaci ya yi da za mu ci gaba da tafiya tare wajen gudanar da harkokin mulki domin ci gaban Nijeriya.

 “Mutane a fadin kasar nan suna sa rai sosai daga gare mu. Suna son mu sauke nauyinsu na tattalin arziki. Suna son mu kawar da rashin tsaro domin manomanmu na karkara su je gonakinsu su noma abincin da muke ci.”

“Mutanenmu sun zuba mana ido mu gyara arzikin kasarmu da kuma kawar da duk wani shingen da ke hana ci gaba. Duk wadannan za mu iya yi ne kadai idan muka jajirce. Za mu iya cimma dukkan kyawawan abubuwan da muka alkawarta a lokacin yakin neman zabe idan muka yi aiki tare cikin jituwa da mutunta hakkinmu da kuma maslahar kasarmu.

“Ba za mu yi watsi da wannan damar ba saboda ‘yan Nijeriya suna son mu yi amfani da kowace rana a cikin shekaru hudu masu zuwa. A bisa lamarin gaskiya, mutanenmu suna son mu rubayya kokarin gwamnatinmu. Hakika sun cancanci shugabanci nagari mai cike da adalci wanda zai inganta rayuwarsu. Dole ne mu ba su iya abin da zamu iya.

“Zan ci gaba da abokin kowa don samun zaman lafiya da kwanciyar hankali da ci gaban Nijeriya. Ina kira ga shugabannin majalisar dokoki ta kasa ta 10 da dukkan ‘yan majalisa su yi aiki tare da ni a wannan tafiya ta gwamnati.”

Tinubu
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
Tambarin Dimokuradiyya

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
makarfi
Tambarin Dimokuradiyya

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Next Post
Idan Ruwan Dagwalon Nukiliya Bai Gurbata Ba, Me Yasa Japan Ba Ta Ajiye Shi Ba?

Idan Ruwan Dagwalon Nukiliya Bai Gurbata Ba, Me Yasa Japan Ba Ta Ajiye Shi Ba?

LABARAI MASU NASABA

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.