ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, November 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hutun Haihuwa: An Samu Masu Yin Tazara 28,561 A Farkon 2023 A Jihar Gombe

by Yunusa Isa
2 years ago
Gombe

Hukumar Lafiya a Matakin Farko ta Jihar Gombe, ta bayyana cewa an samu qaruwar sabin masu yin tazarar haihuwa a jihar, da kimanin mutane 28,561 daga watan Janairu zuwa Maris xin 2023.

Ko-odinetar sashin tazarar haihuwa a hukumar Grace Mabudi ce ta bayyana hakan yayin taron rubu’i na biyu na qungiyar ƴan jarida masu aiki da qungiyar The Challenge Initiative (TCI) kan tazarar haihuwa a jihar.

  • Gwamnan Gombe Ya Nada Njodi Sakataren Gwamnati, Misilli Daraktan Yada Labarai
  • Rukuni Na 3 Na Alhazan Gombe Zasu Tashi Zuwa Madina A Yau Juma’a

Grace ta ce “Qaruwar bata rasa nasaba da jajircewar da kafofin watsa labarai da qungiyoyin ci gaba suke yi wajen wayar da kan jama’a musamman iyalai kan mahimmancin tazarar haihuwa. Gaskiya kuna qoƙari”.

ADVERTISEMENT

Sai dai ta yi qira ga ’ya’yan qungiyar su qara himma wajen qiran a qara samar da kayan da ake amfani da su wajen gudanar da wassu hanyoyin na tazarar haihuwa, wanda shi ne babban qalubalen dake fuskantar ayyukan tazarar a jihar.

A cewarta, jihar tana da wadatatun magungunan tazara, amma tana fama da qarancin kayan da ake amfani da su kamar su auduga, da sirinji, da safar hannu, filasta da sauransu, tana mai tabbatar da cewa dole sai da kayayyakin kafin a iya gudanar da wasu nau’o’in na tazarar haihuwa.

LABARAI MASU NASABA

Sauya Sheƙa: Yadda APC Ke Ci Gaba Da Hamɓarar Da Jam’iyyun Adawa A Majalisa

Kotu Ta Sake Hana PDP Gudanar Da Babban Taronta Na Ƙasa

Tace “qarancin kayayyakin ya sanya ma’aikatan lafiya suna karvar wassu yan kuxaxe daga masu zuwa tazarar ɗin sayar musu nasu da suka tanadar”.

Don haka ko’odinetar ta yi qira ga kungiyoyi masu bada gudunmawa da abokan hulxar ci gaba su qara samar da kayayyakin, lamarin da tace zai qara qarfafa gwiwar mata su riqa yin tazarar ta haihuwa a jihar.

Ko’odinetar wacce ta samu wakilcin mataimakiyar ta Mrs Aise Fada, ta ce asibitoci 456 ne ke yin ayyukan na tazarar haihuwa a faxin jihar.

Ko’odinetar ta ce wata qungiya mai fafutukar bunqasa lafiyar iyali za ta ziyarci jihar don gabatar da wata sabuwar hanyar tazarar haihuwa inda mace zata yiwa kanta allurar tazarar.

Ta ce za a koyawa mata yadda ake yin allurar, don su riqa yinta da kansu.

Grace Mabudi ta ce qungiyar zata horar da manyan jami’ai da masu sa kai na cikin al’umma, waxanda zasu ci gaba da ilimantar da sauran jama’a tare da koya wa mata yadda ake amfani da sabuwar dabarar.

Da take bayyana cewa sabon tsarin kyauta ne, Grace ta ce “Allurar ba ta da wani illa kuma kowane yi xaya yana aiki ne na tsawon watanni uku”.

Taron na rubu’i-rubu’i na tawagar yan jaridan, wanda qungiyar ta The Challenge Initiative ke tallafawa, yana nazari kan ayyukan baya da aka gudanar, da tsara sabbin dabaru kan yadda za a bunqasa tazarar a tsakanin matan jihar.

A nata jawabin, shugabar qungiyar yan jaridan Rabecca Caleb Maina, ta qarfafawa ‘yan qungiyar gwiwa kan su maida hankali kan bada labaran da suka shafi rayuwar al’umma a cikin rahotanninsu na tazarar haihuwa, waxanda zusu jawo hankulan jama’a da kuma bunqasa tazarar a jihar.

Rabecca ta kuma shawarci mambobin qungiyar kan qarin rahotanni daga asibitoci masu zaman kansu, savanin yadda ake yawan maida hankali kan asibitocin gwamnati.

Da take gabatar da wasu ayyukan qungiyar na rubu’i na biyu da suka haxa da rahotanni da labarai da sharhi da wallafe-wallafen da aka yayata kan tazarar haihuwa, shugabar ta ba da tabbacin jajircewar qungiyar wajen qara wayar da kan al’ummar jihar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

APC
Labarai

Sauya Sheƙa: Yadda APC Ke Ci Gaba Da Hamɓarar Da Jam’iyyun Adawa A Majalisa

November 11, 2025
‘Yan Majalisa 60 Sun Yi Barazanar Ficewa Daga PDP
Manyan Labarai

Kotu Ta Sake Hana PDP Gudanar Da Babban Taronta Na Ƙasa

November 11, 2025
Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya
Manyan Labarai

Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya

November 11, 2025
Next Post
An Bude Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Wasa A Turai

An Bude Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Wasa A Turai

LABARAI MASU NASABA

Kofin Duniya 2026 Zai Zama Na Ƙarshe A Wuri Na – Ronaldo 

Kofin Duniya 2026 Zai Zama Na Ƙarshe A Wuri Na – Ronaldo 

November 11, 2025
Jakadun Kasashen Waje: Shirin Raya Kasa Na 15 Na Sin Na Dauke Da Kyakkyawan Sako

Jakadun Kasashen Waje: Shirin Raya Kasa Na 15 Na Sin Na Dauke Da Kyakkyawan Sako

November 11, 2025
APC

Sauya Sheƙa: Yadda APC Ke Ci Gaba Da Hamɓarar Da Jam’iyyun Adawa A Majalisa

November 11, 2025
An Kaddamar Da Babbar Hanyar Mota Da Sin Ta Tallafa Wajen Ginawa A Namibia

An Kaddamar Da Babbar Hanyar Mota Da Sin Ta Tallafa Wajen Ginawa A Namibia

November 11, 2025
‘Yan Majalisa 60 Sun Yi Barazanar Ficewa Daga PDP

Kotu Ta Sake Hana PDP Gudanar Da Babban Taronta Na Ƙasa

November 11, 2025
‘Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Kashe Ɗan Wasan Barau FC A Katsina

‘Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Kashe Ɗan Wasan Barau FC A Katsina

November 11, 2025
Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya

Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya

November 11, 2025
HOTUNA: Yadda Gobara Ta Ƙone Shaguna 25 A Kasuwar Singa A Kano

HOTUNA: Yadda Gobara Ta Ƙone Shaguna 25 A Kasuwar Singa A Kano

November 11, 2025
‘Yan Bindiga Da ‘Yan Ta’adda Sun Fi Sojojin Nijeriya Yawan Makamai – Babachir

‘Yan Bindiga Da ‘Yan Ta’adda Sun Fi Sojojin Nijeriya Yawan Makamai – Babachir

November 11, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Faɗa Ya Kaure Tsakanin Boko Haram Da ISWAP, An Kashe Mayaƙa Sama Da 170

November 11, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.