ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Bude Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Wasa A Turai

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
Turai

LABARAI MASU NASABA

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

An bude kasuwar saye da sayar da ‘yan kwallo a Ingila daga ranar Laraba 14 ga watan Yunin shekara ta 2023 zuwa 1 ga watan Satumbar 2023 kamar yadda aka saba yi duk shekara.

Kungiya za ta iya sayen dan wasan da bashi da yarjejeniya da wata kungiya, haka kuma za’a iya daukar aron dan wasa bisa kan doka da kulla kwantiragi bisa tsarin hukumar kwallon kafa ta duniya.

  • Mace Aba Ce Mai Daraja, Ba Sai Ta Ba Da Kanta Ba Za Ta Yi Suna A Fim – Jamila Saleh
  • Gwamnatin Neja Za Ta Fito Da Tsarin Ci gaban Jihar Na Shekaru 30

Haka kuma kungiya za ta iya daukar aron mai tsaron raga da zarar ba wani babban mai tsaron da yake da lafiya a kasa haka kuma za’a iya ciniki tsakanin kungiyoyin Premier League da ta EFL.

Kasuwar cinikayyar ‘yan kwallo a Ingila ta fara hada-hada daga ranar Laraba 14 ga watan Yunin 2023 zuwa 1 ga watan Satumbar 2023 kuma za’a iya kara wa’adi a karshen ranar rufe kasuwar idan an kusa kammala wani cinikin ko daukar aron dan wasa, amma lokaci bai ba da ikon cimma matsaya ba.

A Faransa kuma tun daga ranar 19 ga watan Yuni kasuwar ‘yan kwallo za ta fara ci a gasar Ligue 1 da sauran wasannin, wadda za ta karkare ranar 1 ga watan Satumbar 2023.

Sannan a kasashen Sipaniya da Jamus da Italiya kasuwar cinikayyar ‘yan kwallo a La Liga da Bundesliga da kuma Serie A za ta fara ci daga ranar 1 ga watan Yuli haka kuma za’a karkare hada-hada ranar 1 ga watan Satumbar 2023.

A kasar Amurka kuwa tuni aka ci kasuwar kwallon kafar Amurka daga 31 ga watan Janairun 2023 zuwa 24 ga watan Afirilun 2023 sannan za’a sake bude kasuwar daga 5 ga watan Yuli zuwa 2 ga watan Agustan 2023.

Ana fara kakar kwallon kafar Amurka daga 25 ga watan Fabrairu, wadda za ta rufe ranar 21 ga watan Oktoban 2023 wanda hakan yake nufin ba tare ake tafiya tsakanin Amurka da nahiyar turai ba.

Can kuwa a kasashen Argentina da Brazil tuni aka ci kasuwar cinikayyar ‘yan kwallo a Brazil, ana sa ran za’a sake yin hada-hada daga 14 ga watan Yuli zuwa 13 ga watan Agustan 2023.

An rufe kasuwar ranar 2 ga watan Fabrairun 2023, sai dai ba a bayyana ranar da za’a sake bude ta ba, amma ana sa ran sake cinikayya a cikin Yunin 2023 kamar yadda aka saba.

A Australia ma kasuwar cinikin ‘yan kwallo a Australia ta ci daga cikin Oktoba zuwa Mayu sannan za kuma a sake bude kasuwar daga 24 ga watan Yulin 2023 zuwa 15 ga watan Oktoban 2023.

Turai
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Ka San Dalilin Da Ya Sa Chana Da Indiya Ba Sa Buga Kofin Duniya?
  • Abba Ibrahim Wada
    Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji
  • Abba Ibrahim Wada
    Lampard Zai Ci Gaba Da Zama A Coventry City
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64
Wasanni

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

July 12, 2026
Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare
Wasanni

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

July 11, 2026
Wasanni

Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu

July 11, 2026
Next Post
Sarkin Musulmi Ya Sanar Da Ranar Asabar A Matsayin Ranar 1 Ga Muharram Na Shekarar 1444

An Bukaci Musulman Nijeriya Su Fara Duban Watan Babbar Sallah Yau Lahadi

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.