• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

“Zaman Lafiya Ta Hanyar Tattaunawa” Ita Ce Kawai Mafita Ga Gabas Ta Tsakiya

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
“Zaman Lafiya Ta Hanyar Tattaunawa” Ita Ce Kawai Mafita Ga Gabas Ta Tsakiya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar 14 ga watan Yuni, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya tattauna da shugaban Falasdinu Mahmoud Abbas a nan birnin Beijing. Sun sanar da kulla dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare tsakanin Sin da Falasdinu.

Shugaba Xi ya gabatar da shawarwari mai kunshe da abubuwa uku na warware batun Falasdinu. Ya bayyana cewa babbar hanyar warware batun Falasdinawa ita ce kafa kasar Falasdinu mai cin gashin kanta wacce ke da cikakken ikon mallakar kai a bisa yarjejeniyar kan iyakoki ta shekarar 1967 da kuma gabashin Kudus a matsayin babban birninta.

  • Shugaba Xi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Ya kamata a biya bukatun tattalin arziki da rayuwar Falasdinawa, sannan kasashen duniya su kara kaimi wajen taimakon raya kasa da taimakon jin kai ga Falasdinu. Kuma a karshe, yana da muhimmanci a kiyaye hanyar da ta dace na tattaunawar da za ta kai ga zaman lafiya.

Hanyar da kasar Sin ke bi na samun zaman lafiya ta samo asali ne daga tsohuwar hikimar kasar Sin, kamar yadda yake bayyane a cikin wadannan kalamai: “Bai kamata masu karfi da masu kudi su rika zaluntar marasa karfi da matalauta ba”, kuma “duk kasar da ke takama da karfin yaki, duk girmanta, daga karshe za ta durkushe.” Wadannan kalmomi masu zurfi suna misalta kimar kasar Sin yayin da take tafiyar da tsarin kasa da kasa mai sarkakiya da rashin kwanciyar hankali, tare da neman hanyar zaman lafiya da ci gaba, ta hanyar tattaunawa da mutunta ’yancin juna ba tare da katsalandan ko shisshigi ba.

Abin da ke tattare da irin wannan yunkurin na kasar Sin shi ne wasu suka mayar da batun tattaunawa game da babbar hamayya tsakanin manyan tattalin arzikin duniya guda biyu. A wannan yanayi, an mayar da hankali kan Sin da Amurka a Gabas ta Tsakiya, da tabarbarewar alakar da ke tsakaninsu. Sanin kowa ne cewa Amurka da Isra’ila sun kulla alaka mai karfi ta tsaro, da tattalin arziki da siyasa.

Labarai Masu Nasaba

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Kuma idan aka yi la’akari da yanayin siyasa mai sarkakiya a yankin, yin nazari game da dangantakar abota tsakanin kasar Sin da Falasdinu, wani zai dauka kasar Sin na kalubalantar Amurka ne.

Kasar Sin ba ta da sha’awar kalubalantar Amurka a Gabas ta Tsakiya ko kuma a ko’ina. Tasirin da Amurka ke da shi a yankin na kara raguwa saboda tsarin siyasarta da bukatunta. Babu wanda za a zarga da sanyaya dangantakar Amurka da yankin Gabas ta Tsakiya face zabin da Amurka ta yiwa kanta.

Akidar Confucius ta kayyade cewa “ya kamata mutum ya nemi jituwa a cikin bambance-bambance kuma kada ya yi wa wasu abin da ba zai so a masa ba.” Burin kasar Sin shi ne ta samar da daidaito a wannan duniyar da ke cike da bambance-bambance. Kuma tana taimaka wa kasashen Gabas ta Tsakiya da hakan. (Yahaya Babs)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Maimakon Yaki, Afirka Da Sin Sun Zabi Zaman Lafiya

Next Post

Johann Rupert Ya Doke Dangote A Matsayin Mutumin Da Ya Fi Kowa Kudi A Afirka

Related

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

4 hours ago
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu
Daga Birnin Sin

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

5 hours ago
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

6 hours ago
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere
Daga Birnin Sin

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

7 hours ago
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

8 hours ago
Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa
Daga Birnin Sin

Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

10 hours ago
Next Post
Johann Rupert Ya Doke Dangote A Matsayin Mutumin Da Ya Fi Kowa Kudi A Afirka

Johann Rupert Ya Doke Dangote A Matsayin Mutumin Da Ya Fi Kowa Kudi A Afirka

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.