• English
  • Business News
Thursday, October 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wang Yi Da Qin Gang Sun Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

by CMG Hausa
2 years ago
Wang yi

Wang Yi, darektan ofishin kula da harkokin waje na kwamitin tsakiya na jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, ya gana da sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken a yau Litinin a nan birnin Beijing, inda ya yi kira da a yi kokarin gyara dangantakar kasashen Sin da Amurka wadda ta yi tsami.

Wang ya ce ziyarar ta Blinken a nan Beijing ta zo ne a wani muhimmin lokaci a dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, inda ake bukatar zabi tsakanin tattaunawa ko gwabzawa, hadin gwiwa ko rikici.

  • Ministan Harkokin Kasuwanci na Sin Wang Wentao Ya Gana Da Darakta Janar Ta WTO Ngozi Okonjo-Iweala

Lura da cewa lokaci na tafiya haka ma alakar dake tsakanin Sin da Amurka. Wang ya ce canza tarihi ba zai yi tasiri ga makoma ba, haka ma wargaza dangantakar dake tsakanin kasashen biyu don a sake gina sabuwa.

Ya ce, “Dole ne mu nuna kyakkyawar hali ga jama’a, da tarihi da kuma duniya baki daya, tare da gyara dangantakar da ke tsakanin Sin da Amurka.” Ya yi kira ga bangarorin biyu da su maido da huldar da ke tsakanin kasashen biyu zuwa tafarkin da ya dace, da kuma samar da hanya madaidaiciya ga Sin da Amurka don samun jituwa a sabon zamani.

A jiya ne, mamban majalisar gudanarwar kasar Sin kuma ministan harkokin wajen kasar Qin Gang ya gana da sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken dake ziyara a nan birnin Beijing.

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

Shugabannin Kasashe Da Dama Sun Yaba Wa Sin Kan Gudummawar Da Ta Bayar A Fannin Tabbatar Da Daidaiton Jinsi

A yayin shawarwarin, Qin Gang ya bayyana cewa, yanzu dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka ta gamu da matsala mafi tsanani bayan da kasashen biyu suka kulla dangantakar diflomasiyya a tsakaninsu, wannan bai dace da moriyar jama’ar kasashen biyu da begen kasa da kasa ba. Sin tana yin kokarin raya dangantakar dake tsakaninta da kasar Amurka ta zaman lafiya da amfani, Sin tana fatan kasar Amurka za ta maida hankali ga kasar Sin bisa hakikanin yanayi, da yin kokari tare da kasar Sin, da tabbatar da tushen siyasa na raya dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, da daidaita matsaloli ba zato ba tsammani cikin lumana yadda ya kamata. Kana kasashen biyu ya kamata su aiwatar da ayyukan da shugabannin kasashen biyu suka cimma a tsibirin Bali, da sa kaimi ga maido da dangantakarsu.

Qin Gang ya bayyana matsayin kasar Sin kan manyan batutuwan dake shafar moriyar kasar Sin, ciki har da batun yankin Taiwan, ya kalubalanci bangaren kasar Amurka da ya bi ka’idar Sin daya tak a duniya da hadaddun rahotanni uku da Sin da Amurka suka daddale, da cika alkawarinta na kin amincewa da ‘yancin yankin Taiwan.

Hakazalika kuma, bangarorin biyu sun zurfafa mu’amala da juna kan yadda za a raya dangantakar dake tsakaninsu da manyan batutuwan da abin ya shafa. (Mai Fassarawa: Zainab Zhang&Yahaya Babs)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

October 16, 2025
Shugabannin Kasashe Da Dama Sun Yaba Wa Sin Kan Gudummawar Da Ta Bayar A Fannin Tabbatar Da Daidaiton Jinsi
Daga Birnin Sin

Shugabannin Kasashe Da Dama Sun Yaba Wa Sin Kan Gudummawar Da Ta Bayar A Fannin Tabbatar Da Daidaiton Jinsi

October 16, 2025
Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori
Daga Birnin Sin

Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori

October 16, 2025
Next Post
Wang yi

Tinubu Ya Kori Shugabannin Gudanarwar Ma'aikatu Da Hukumomin Gwamnati

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

October 16, 2025
Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

October 16, 2025
Shugabannin Kasashe Da Dama Sun Yaba Wa Sin Kan Gudummawar Da Ta Bayar A Fannin Tabbatar Da Daidaiton Jinsi

Shugabannin Kasashe Da Dama Sun Yaba Wa Sin Kan Gudummawar Da Ta Bayar A Fannin Tabbatar Da Daidaiton Jinsi

October 16, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisar Dattawa Ta Amince Da Amupitan A Matsayin Shugaban INEC

October 16, 2025
Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori

Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori

October 16, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Fursunoni Bayan Kammala Zaman Kurkuku

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Fursunoni Bayan Kammala Zaman Kurkuku

October 16, 2025
Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 16, 2025
Majalisar Dattawa Ta Fara Tantance Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Majalisar Dattawa Ta Fara Tantance Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 16, 2025
An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

October 16, 2025
Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu

Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu

October 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.