ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wang Yi Da Qin Gang Sun Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

by CMG Hausa
3 years ago
Wang yi

Wang Yi, darektan ofishin kula da harkokin waje na kwamitin tsakiya na jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, ya gana da sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken a yau Litinin a nan birnin Beijing, inda ya yi kira da a yi kokarin gyara dangantakar kasashen Sin da Amurka wadda ta yi tsami.

Wang ya ce ziyarar ta Blinken a nan Beijing ta zo ne a wani muhimmin lokaci a dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, inda ake bukatar zabi tsakanin tattaunawa ko gwabzawa, hadin gwiwa ko rikici.

  • Ministan Harkokin Kasuwanci na Sin Wang Wentao Ya Gana Da Darakta Janar Ta WTO Ngozi Okonjo-Iweala

Lura da cewa lokaci na tafiya haka ma alakar dake tsakanin Sin da Amurka. Wang ya ce canza tarihi ba zai yi tasiri ga makoma ba, haka ma wargaza dangantakar dake tsakanin kasashen biyu don a sake gina sabuwa.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Dole ne mu nuna kyakkyawar hali ga jama’a, da tarihi da kuma duniya baki daya, tare da gyara dangantakar da ke tsakanin Sin da Amurka.” Ya yi kira ga bangarorin biyu da su maido da huldar da ke tsakanin kasashen biyu zuwa tafarkin da ya dace, da kuma samar da hanya madaidaiciya ga Sin da Amurka don samun jituwa a sabon zamani.

A jiya ne, mamban majalisar gudanarwar kasar Sin kuma ministan harkokin wajen kasar Qin Gang ya gana da sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken dake ziyara a nan birnin Beijing.

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

A yayin shawarwarin, Qin Gang ya bayyana cewa, yanzu dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka ta gamu da matsala mafi tsanani bayan da kasashen biyu suka kulla dangantakar diflomasiyya a tsakaninsu, wannan bai dace da moriyar jama’ar kasashen biyu da begen kasa da kasa ba. Sin tana yin kokarin raya dangantakar dake tsakaninta da kasar Amurka ta zaman lafiya da amfani, Sin tana fatan kasar Amurka za ta maida hankali ga kasar Sin bisa hakikanin yanayi, da yin kokari tare da kasar Sin, da tabbatar da tushen siyasa na raya dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, da daidaita matsaloli ba zato ba tsammani cikin lumana yadda ya kamata. Kana kasashen biyu ya kamata su aiwatar da ayyukan da shugabannin kasashen biyu suka cimma a tsibirin Bali, da sa kaimi ga maido da dangantakarsu.

Qin Gang ya bayyana matsayin kasar Sin kan manyan batutuwan dake shafar moriyar kasar Sin, ciki har da batun yankin Taiwan, ya kalubalanci bangaren kasar Amurka da ya bi ka’idar Sin daya tak a duniya da hadaddun rahotanni uku da Sin da Amurka suka daddale, da cika alkawarinta na kin amincewa da ‘yancin yankin Taiwan.

Hakazalika kuma, bangarorin biyu sun zurfafa mu’amala da juna kan yadda za a raya dangantakar dake tsakaninsu da manyan batutuwan da abin ya shafa. (Mai Fassarawa: Zainab Zhang&Yahaya Babs)

Wang yi
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Next Post
Wang yi

Tinubu Ya Kori Shugabannin Gudanarwar Ma'aikatu Da Hukumomin Gwamnati

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.