ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wang Yi Da Qin Gang Sun Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

by CMG Hausa
3 years ago
Wang yi

Wang Yi, darektan ofishin kula da harkokin waje na kwamitin tsakiya na jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, ya gana da sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken a yau Litinin a nan birnin Beijing, inda ya yi kira da a yi kokarin gyara dangantakar kasashen Sin da Amurka wadda ta yi tsami.

Wang ya ce ziyarar ta Blinken a nan Beijing ta zo ne a wani muhimmin lokaci a dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, inda ake bukatar zabi tsakanin tattaunawa ko gwabzawa, hadin gwiwa ko rikici.

  • Ministan Harkokin Kasuwanci na Sin Wang Wentao Ya Gana Da Darakta Janar Ta WTO Ngozi Okonjo-Iweala

Lura da cewa lokaci na tafiya haka ma alakar dake tsakanin Sin da Amurka. Wang ya ce canza tarihi ba zai yi tasiri ga makoma ba, haka ma wargaza dangantakar dake tsakanin kasashen biyu don a sake gina sabuwa.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Dole ne mu nuna kyakkyawar hali ga jama’a, da tarihi da kuma duniya baki daya, tare da gyara dangantakar da ke tsakanin Sin da Amurka.” Ya yi kira ga bangarorin biyu da su maido da huldar da ke tsakanin kasashen biyu zuwa tafarkin da ya dace, da kuma samar da hanya madaidaiciya ga Sin da Amurka don samun jituwa a sabon zamani.

A jiya ne, mamban majalisar gudanarwar kasar Sin kuma ministan harkokin wajen kasar Qin Gang ya gana da sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken dake ziyara a nan birnin Beijing.

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

A yayin shawarwarin, Qin Gang ya bayyana cewa, yanzu dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka ta gamu da matsala mafi tsanani bayan da kasashen biyu suka kulla dangantakar diflomasiyya a tsakaninsu, wannan bai dace da moriyar jama’ar kasashen biyu da begen kasa da kasa ba. Sin tana yin kokarin raya dangantakar dake tsakaninta da kasar Amurka ta zaman lafiya da amfani, Sin tana fatan kasar Amurka za ta maida hankali ga kasar Sin bisa hakikanin yanayi, da yin kokari tare da kasar Sin, da tabbatar da tushen siyasa na raya dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, da daidaita matsaloli ba zato ba tsammani cikin lumana yadda ya kamata. Kana kasashen biyu ya kamata su aiwatar da ayyukan da shugabannin kasashen biyu suka cimma a tsibirin Bali, da sa kaimi ga maido da dangantakarsu.

Qin Gang ya bayyana matsayin kasar Sin kan manyan batutuwan dake shafar moriyar kasar Sin, ciki har da batun yankin Taiwan, ya kalubalanci bangaren kasar Amurka da ya bi ka’idar Sin daya tak a duniya da hadaddun rahotanni uku da Sin da Amurka suka daddale, da cika alkawarinta na kin amincewa da ‘yancin yankin Taiwan.

Hakazalika kuma, bangarorin biyu sun zurfafa mu’amala da juna kan yadda za a raya dangantakar dake tsakaninsu da manyan batutuwan da abin ya shafa. (Mai Fassarawa: Zainab Zhang&Yahaya Babs)

Wang yi
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
Wang yi

Tinubu Ya Kori Shugabannin Gudanarwar Ma'aikatu Da Hukumomin Gwamnati

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.