• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sarkin Noman Gaya Ya Nemi Gwamna Abba Ya Bullo Da Sabon Tsarin Bunkasa Noma

by Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Sarkin Noman Gaya Ya Nemi Gwamna Abba Ya Bullo Da Sabon Tsarin Bunkasa Noma
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shawarar mu ga gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusif Abba Gida-Gida ita ce a yi wa manoman Kano sabon tsarin bunkasa noma a zamanin mulkinsa wanda manoman ba za su taba mantawa da shi ba kamar aikin marigayi Alhaji Audu Bako.

Wannan bayanin ya fito ne daga bakin Sarkin Noman Masarautar Gaya, Alhaji Ibrahim Yakubu Tagahu a zantawarsa da wakilinmu.
Ya ci gaba da cewa, “domin Kano dai na da ginshikai, kamar Ilimi, Karatu, Noma, Sarauta, Kasuwanci, kuma akasarin mutanan Kano manoma ne da `yan kasuwa kuma yanzu haka an kiyasta Kano tana da albarkar yawan jama`a da suka kai kimanin Miliyan 20 a kiyasi, duk da rabon Kano da kidayar jama`a tun shekarar 2006 yau kimani shekara 17 kenan wanda ina ganin cewa a kiyasin muna da manoma a Kano za su haura miliyan 15 wanda ka ga sunfi yawan mutanan wasu kasashe da dama a duniya a mahangar mu ta manoma da mu ke zama a yankunan karkara.

  • Ban Yi Nadamar Rusau A Kano Ba -Gwamnan Kano

Bayan ya yi murnar kammala zaban shugaban kasa da na `yan majalisar dattawa da na wakilai na tarayya da na jihohi da kuma gwamnoni lafiya a Nijeriya, Alhaji Ibrahim ya ce abin da yake kara faranta musu rai game da zaben shi ne, “a ciki ne aka zabi mai girma gwamnan Jahar Kano Injiniya Abba Kabir Yusif Abba Gida- Gida wanda kuma danmu ne kuma jikanmu ne idan aka yi la`akari da tarihin sabon gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusif mai alaka ko tarihi da masarautar Gaya da ta Kano baki daya.”

Ya kara da cewa, “Babu shakka kowa ya san Kano kasa ce mai albarkar noma da fadin kasa mai karbar shuka kowa ne iri na duniya a kyakkyawan zato na idan aka shuka shi a Kano za yi bisa la`akari da shuke-shuken da mu ke na rani da na damina tun daga kan Dawa, Gero, Masara, Shinkafa, Dauro, Maiwa, Wake, Gyada, Waken suya, Accha,Alkama a noman rani, da sauran nau`o`i iri-iri na kayan abinci mai kwaya.

“Haka kuma a Kano ana noman gyada wanda Kano na noma gyada a kalla 60 cikin 100 na noman gyada a Nijeriya muna noman auduga duk a noman damuna a Kano a na noman Rogo, Makani, Gwaza, haka a na noman dankali a Kano, ana noma Albasa, yakuwa, Doborodo, Rama, Zogale, da sauransu haka a Kano ne ake noman rake noman takanda, haka a laiyahu da dai sauransu wanda wadannan abubuwa idan aka samu tsari na gwamnatin Kano ko ta tarayya a gona daya za a iya samar wa miliyoyin matasa aikin yi wanda za a dogara da kai ba tare da ragaita zuwa ofis ko kamfanoni neman aiki ba. Wannan kuma ba zai yiwu ba sai da kyakkawan tsari na gwamnatin Kano ta Abba Gida-Gida koma ta gwamnatin tarayya karkashin Shugaban Kasa Ahmad Bola Tunubu.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

Da ya juya kan matsalolin manoman Kano kuwa, Sarkin Noman na Gaya ya ce, “Kadan daga cikin Matsalolin manoman Kano da mu ke son a kawo mana kyakkyawan tsari na tallafa mana akwai karancin motocin noma da kayan aiki na zamani karancin guraran noman rani bisa la`akari da yadda Kano ta ke da dam-dam wato madatsun ruwa wanda aka gina su tun zamanin marigayi Audu Bako tun lokacin da Kano ta zama jiha a shekarar 1966 suke wanda suna da bukatar a yashe su a tsattsaga su domin fadada gurin noma ga dimbin matasanmu na Kano.

“Haka tsarin tallafa wa manoma duk lokacin da gwamnatin Abba Gida-Gida za ta yi ko ta Tunubu, wajibi ne a samo a halin abun kamar manoma, da shugabannin su da sarakunan su, da kuma sarakuna iyayen al`umma da sauran shugaban ni wanda al`umma ke ganin kimarsu amma sanya siyasa wajan raba tallafin noma mu dai manoma na gaskiya ba ma amfana da wannan tsari kuma yau manoma na fama da tsadar taki, tsadar irin, tsadar maganin ciyawa, da sauran kayayyaki da manoma su ke amfani da su yau sun yi tsada wanda a neman kyakkyawan tsari na tallafa wa manoman Kano dan bunkasawa.

“Haka zalika shawarar mu duk wanda za a bawa kwamishina na ma`aikatar gona da sauran shugabanci na KASCO Da KANARDA da sauran cibiyoyin bunkasa noma a Kano a bawa wanda ya san harkar, mai kishin harkar, hakan zai taimaka wa mu manoma haka kuma mu na yaba wa sabon gwamnan Kano kan kishinsa na ilimi, lafiya, tattalin arziki, kasuwanci, ruwan sha, Taswiyyarar Kano, Tsaro, Samar da aikin yi ga matasa da dai sauransu kan yadda muka ga ya himmatu da hawansa gwamnan Kano.” In ji shi.

A karshe, sarkin noman masarautar noman Gaya Alhaji Ibrahim Yakubu Tagahu, ya ce “a madadan sarkin Gaya Dr. Ibrahim Abdulkadir muna yi wa Alhazan bana da suka sauke farali da mu wadanda muka yi Sallar Layya, muna yi wa masarautar Gaya, masarautar Kano, da Jihar Kano da Nijeriya fatan samun wadataccan tsaro da zaman lafiyar al`ummar Nijeriya baki daya.” Ya bayyana.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin: Ya Dace Amurka Ta Ingiza Hada Kan UNESCO Bayan Dawowarta Hukumar

Next Post

Gwamnatin Kano Za Ta Bincike Dakatar Da Albashin Ma’aikatan Kano 

Related

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

12 hours ago
Neja
Noma Da Kiwo

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

19 hours ago
Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani
Noma Da Kiwo

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

1 week ago
Gwamnonin Arewa Na Kokarin Farfado Da Hadin Kan Yankin
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

1 week ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Nau’ikan Amfanin Gona Da Ke Saurin Girma Cikin ‘Yan Watanni

1 week ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Sama Wa Manoma Masu Renon Tsirrai Rancen Kudi

2 weeks ago
Next Post
Gwamnatin Kano Za Ta Bincike Dakatar Da Albashin Ma’aikatan Kano 

Gwamnatin Kano Za Ta Bincike Dakatar Da Albashin Ma'aikatan Kano 

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.