• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hajji 2023: Tinubu Ya Bukaci Alhazai Da Su Kara Hakuri Da Halin Matsi Da Takura Da Suke Ciki

by Muhammad
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Tinubu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaba Tinubu ya yi kira ga alhazan Nijeriya da suka je aikin hajjin bana a kasar Saudiyya da su kwantar da hankalinsu, yana mai cewa abu mai muhimmaci a aikin Hajji shi ne hakuri da sadaukarwa a cikin wahalhalu.

Jakadan Nijeriya a kasar Saudiyya, Ambasada Yahaya Lawal, ne ya isar da sakon shugaban ga alhazan Nijeriya yayin ziyarar da ya kai tantin maniyyatan a Mina a Alhamis.

  • Mahajjatan Nijeriya Sun Yi Wa Ƙasa Addu’o’i Na Musamman A Filin Arfa
  • Mahajjata Sama Da Miliyan 2 Ne Za Su Yi Aikin Hajjin Bana

Wakilin Nijeriya wanda ya samu rakiyar takwaransa na kasar Sudan, Ambasada Safiu Olaniyan, shugaban hukumar alhazai ta Nijeriya (NAHCON), Alhaji Zikrullah Kunle Hassan, da kwamishinoninsa da manyan jami’an hukumar NAHCON, ya bukaci alhazan Nijeriya da su ci gaba da gudanar da aikin hajjinsu na bana cikin tsari da zama jakadu nagari na kasarsu a lokacin da suke kasa mai tsarki.

Shugaba Tinubu ya kuma shawarci mahajjatan da cewa, maimakon yin gunaguni game da kalubalen da suke fuskanta, ya kamata su mai da hankali kan muhimmancin tafiya kasa mai tsarki tare da mayar da hankali wajen yi wa Nijeriya addu’a, yana mai cewa kasar na bukatar addu’o’insu don shawo kan kalubalenta.

“Yanzu haka an sanar da shugaban kasar kan irin kyawawan dabi’un da kuka nuna kuma yana fatan ku ci gaba da wakiltar Nijeriya da kyau a kasa mai tsarki. Sannan ku sanya Nijeriya cikin addu’o’in ku, mun san kalubalen da kasarmu ke fuskanta kuma yana da muhimmanci ku yi amfani da wannan dama ta musamman wajen yin addu’a ta musamman don ci gaban Nijeriya, zaman lafiya, kwanciyar hankali da walwala ga ‘Yan Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

“Muna godiya da goyon bayanku, kuma muna mika godiyarku ga shugaban hukumar NAHCON bisa yadda ya samar da shugabanci na gari, muna fatan shugabannin su ci gaba da gudanar da ayyukan alheri da suke yi har sai dukkan alhazai sun dawo gida lafiya.” Cewar Lawal.

Tun da farko, shugaban NAHCON, Alhaji Zikrullah Kunle Hassan, ya ce makasudin ziyarar ita ce ziyarar mahajjata tare da ganin abubuwan da suka faru a aikin Hajji a wurare masu tsarki musamman a Mina, Arafat. da Muzdalifa da ayyukan Hajji baki daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Aikin HajjiAlhazaiHajji 2023Hajjin BanaMahajjataTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Fitaccen Likitan Nan Dan Jihar Bauchi Farfesa Abdu Ya Rasu

Next Post

Goron Sallah

Related

An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

22 minutes ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

3 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

4 hours ago
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Manyan Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

4 hours ago
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu
Manyan Labarai

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

9 hours ago
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki
Manyan Labarai

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

20 hours ago
Next Post
Goron Sallah

Goron Sallah

LABARAI MASU NASABA

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

June 28, 2025
Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

June 28, 2025
Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

June 28, 2025
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Ƙoƙarin Ƙungiyoyin Afrika A Gasar Kofin Duniya

June 28, 2025
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

June 28, 2025
Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.