ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hajji 2023: Tinubu Ya Bukaci Alhazai Da Su Kara Hakuri Da Halin Matsi Da Takura Da Suke Ciki

by Muhammad
3 years ago
Tinubu

Shugaba Tinubu ya yi kira ga alhazan Nijeriya da suka je aikin hajjin bana a kasar Saudiyya da su kwantar da hankalinsu, yana mai cewa abu mai muhimmaci a aikin Hajji shi ne hakuri da sadaukarwa a cikin wahalhalu.

Jakadan Nijeriya a kasar Saudiyya, Ambasada Yahaya Lawal, ne ya isar da sakon shugaban ga alhazan Nijeriya yayin ziyarar da ya kai tantin maniyyatan a Mina a Alhamis.

  • Mahajjatan Nijeriya Sun Yi Wa Ƙasa Addu’o’i Na Musamman A Filin Arfa
  • Mahajjata Sama Da Miliyan 2 Ne Za Su Yi Aikin Hajjin Bana

Wakilin Nijeriya wanda ya samu rakiyar takwaransa na kasar Sudan, Ambasada Safiu Olaniyan, shugaban hukumar alhazai ta Nijeriya (NAHCON), Alhaji Zikrullah Kunle Hassan, da kwamishinoninsa da manyan jami’an hukumar NAHCON, ya bukaci alhazan Nijeriya da su ci gaba da gudanar da aikin hajjinsu na bana cikin tsari da zama jakadu nagari na kasarsu a lokacin da suke kasa mai tsarki.

ADVERTISEMENT

Shugaba Tinubu ya kuma shawarci mahajjatan da cewa, maimakon yin gunaguni game da kalubalen da suke fuskanta, ya kamata su mai da hankali kan muhimmancin tafiya kasa mai tsarki tare da mayar da hankali wajen yi wa Nijeriya addu’a, yana mai cewa kasar na bukatar addu’o’insu don shawo kan kalubalenta.

“Yanzu haka an sanar da shugaban kasar kan irin kyawawan dabi’un da kuka nuna kuma yana fatan ku ci gaba da wakiltar Nijeriya da kyau a kasa mai tsarki. Sannan ku sanya Nijeriya cikin addu’o’in ku, mun san kalubalen da kasarmu ke fuskanta kuma yana da muhimmanci ku yi amfani da wannan dama ta musamman wajen yin addu’a ta musamman don ci gaban Nijeriya, zaman lafiya, kwanciyar hankali da walwala ga ‘Yan Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

“Muna godiya da goyon bayanku, kuma muna mika godiyarku ga shugaban hukumar NAHCON bisa yadda ya samar da shugabanci na gari, muna fatan shugabannin su ci gaba da gudanar da ayyukan alheri da suke yi har sai dukkan alhazai sun dawo gida lafiya.” Cewar Lawal.

Tun da farko, shugaban NAHCON, Alhaji Zikrullah Kunle Hassan, ya ce makasudin ziyarar ita ce ziyarar mahajjata tare da ganin abubuwan da suka faru a aikin Hajji a wurare masu tsarki musamman a Mina, Arafat. da Muzdalifa da ayyukan Hajji baki daya.

Tinubu
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Yadda Na Tsira Daga Cutar Mashaƙo A Katsina: “Na Fara Da Tsartuwar Jini Tare Da Yawu”
  • Muhammad
    An Naɗa Yusuf Nasidi Nasir A Matsayin Talban Barayan Kano
  • Muhammad
    Wani Kamfani Ya Tallafa Wa Masu Sana’ar Shayi A Kano
  • Muhammad
    Kosan Waka Ya Rasu, Gwamnan Kano Ya Jajanta Wa Iyalansa

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
Goron Sallah

Goron Sallah

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.