• English
  • Business News
Wednesday, July 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hajji 2023: Tinubu Ya Bukaci Alhazai Da Su Kara Hakuri Da Halin Matsi Da Takura Da Suke Ciki

by Muhammad
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Tinubu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaba Tinubu ya yi kira ga alhazan Nijeriya da suka je aikin hajjin bana a kasar Saudiyya da su kwantar da hankalinsu, yana mai cewa abu mai muhimmaci a aikin Hajji shi ne hakuri da sadaukarwa a cikin wahalhalu.

Jakadan Nijeriya a kasar Saudiyya, Ambasada Yahaya Lawal, ne ya isar da sakon shugaban ga alhazan Nijeriya yayin ziyarar da ya kai tantin maniyyatan a Mina a Alhamis.

  • Mahajjatan Nijeriya Sun Yi Wa Ƙasa Addu’o’i Na Musamman A Filin Arfa
  • Mahajjata Sama Da Miliyan 2 Ne Za Su Yi Aikin Hajjin Bana

Wakilin Nijeriya wanda ya samu rakiyar takwaransa na kasar Sudan, Ambasada Safiu Olaniyan, shugaban hukumar alhazai ta Nijeriya (NAHCON), Alhaji Zikrullah Kunle Hassan, da kwamishinoninsa da manyan jami’an hukumar NAHCON, ya bukaci alhazan Nijeriya da su ci gaba da gudanar da aikin hajjinsu na bana cikin tsari da zama jakadu nagari na kasarsu a lokacin da suke kasa mai tsarki.

Shugaba Tinubu ya kuma shawarci mahajjatan da cewa, maimakon yin gunaguni game da kalubalen da suke fuskanta, ya kamata su mai da hankali kan muhimmancin tafiya kasa mai tsarki tare da mayar da hankali wajen yi wa Nijeriya addu’a, yana mai cewa kasar na bukatar addu’o’insu don shawo kan kalubalenta.

“Yanzu haka an sanar da shugaban kasar kan irin kyawawan dabi’un da kuka nuna kuma yana fatan ku ci gaba da wakiltar Nijeriya da kyau a kasa mai tsarki. Sannan ku sanya Nijeriya cikin addu’o’in ku, mun san kalubalen da kasarmu ke fuskanta kuma yana da muhimmanci ku yi amfani da wannan dama ta musamman wajen yin addu’a ta musamman don ci gaban Nijeriya, zaman lafiya, kwanciyar hankali da walwala ga ‘Yan Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

“Muna godiya da goyon bayanku, kuma muna mika godiyarku ga shugaban hukumar NAHCON bisa yadda ya samar da shugabanci na gari, muna fatan shugabannin su ci gaba da gudanar da ayyukan alheri da suke yi har sai dukkan alhazai sun dawo gida lafiya.” Cewar Lawal.

Tun da farko, shugaban NAHCON, Alhaji Zikrullah Kunle Hassan, ya ce makasudin ziyarar ita ce ziyarar mahajjata tare da ganin abubuwan da suka faru a aikin Hajji a wurare masu tsarki musamman a Mina, Arafat. da Muzdalifa da ayyukan Hajji baki daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Aikin HajjiAlhazaiHajji 2023Hajjin BanaMahajjataTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Fitaccen Likitan Nan Dan Jihar Bauchi Farfesa Abdu Ya Rasu

Next Post

Goron Sallah

Related

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba
Manyan Labarai

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

3 hours ago
Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820
Manyan Labarai

Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

5 hours ago
Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki
Manyan Labarai

Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

6 hours ago
Igbo Ne Ke Aikata Laifuka A Kudu, Ba Fulani Makiyaya Ba – Gwamna Soludo
Manyan Labarai

Igbo Ne Ke Aikata Laifuka A Kudu, Ba Fulani Makiyaya Ba – Gwamna Soludo

16 hours ago
Sauyin Sheƙa Ya Mamaye PDP Da Sauran Jam’iyyu A Borno, Ana Ta Shiga ADC
Manyan Labarai

Sauyin Sheƙa Ya Mamaye PDP Da Sauran Jam’iyyu A Borno, Ana Ta Shiga ADC

17 hours ago
ASUU Ta Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Biya Albashin Watan Yuni
Manyan Labarai

ASUU Ta Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Biya Albashin Watan Yuni

23 hours ago
Next Post
Goron Sallah

Goron Sallah

LABARAI MASU NASABA

An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Babu Wanda Ya Buƙaci Atiku Ka Da Ya Yi Takara A 2027 – ADC

July 9, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Amurka Ta Tsaurara Matakan Bai Wa ‘Yan Nijeriya Biza

July 9, 2025
Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

July 9, 2025
Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

July 9, 2025
Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense

Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense

July 9, 2025
Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

July 9, 2025
Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki

Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki

July 9, 2025
Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai

Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai

July 8, 2025
Firaminsitan Sin: Dole Ne Hadin Gwiwar Brics Ya Gaggauta Kafa Ka’idar Ciniki Da Tattalin Arzikin Duniya Mai Adalci Da Bude Kofa

Firaminsitan Sin: Dole Ne Hadin Gwiwar Brics Ya Gaggauta Kafa Ka’idar Ciniki Da Tattalin Arzikin Duniya Mai Adalci Da Bude Kofa

July 8, 2025
Babatun Lai Ching-Te Ba Zai Taba Girgiza Kasancewar Sin Day Tak A Duniya Ba

Babatun Lai Ching-Te Ba Zai Taba Girgiza Kasancewar Sin Day Tak A Duniya Ba

July 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.