ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mahajjata Sama Da Miliyan 2 Ne Za Su Yi Aikin Hajjin Bana

by Abubakar Abba
3 years ago
Mahajjata

Mahajjata sama da miliyan biyu daga sassa daban-daban na duniya ne da suka isa masarautar Saudiyya domin gudanar da aikin hajjin bana, sun yi dafifi a filin Arafah domin gudanar da ibada muhimmiya.

Alhazan dai tun daga wayewar garin ranar Talata suka fara tafiya Muna daga Makkah zuwa Arafah, Muzdalifah da komawa Muna, hakan ya nuna an fara aikin Hajjin.

  • Matawalle Bai Saci Kudin Jihar Zamfara Ba — Anas Kaura
  • Za Mu Kawar Da Matsalar Tsaro A Nijeriya -Nuhu Ribadu

Ana sa ran mahajjata za su kasance a filin Arafah a yau, daga bayan Sallar La’asar da La’asar zuwa faduwar rana, suna neman gafarar Allah, Rahma, Albarka, shiriya, aminci, kwanciyar hankali, ci gaba da sauran addu’o’i.

ADVERTISEMENT

Ana sa ran Malamai za su jagoranci mahajjatan Nijeriya wajen yin addu’o’in samun zaman lafiya, kwanciyar hankali, ci gaba da ci gaban al’ummar Nijeriya da kuma kasar ta shawo kan dukkan kalubalen da ta ke fuskanta ta fuskar tsaro da siyasa da tattalin arziki.

Bayan faduwar rana alhazai za su tashi zuwa Muzdalifah inda ake sa ran za su kwana kafin su koma Muna bayan an idar da sallar Asubah, domin jifan shaidan.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

A gefe guda kuwa, Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Nijeriya (NAHCON), ta nuna rashin gamsuwarta kan rashin isassun tantuna ga mahajjatan Nijeriya a Muna da Kamfanin Saudiyya ke da alhakin samarwa da isassun tantuna a Mashã’ir ga ‘yan Nijeriya.

Shugaban Hukumar Alhaji Zikrullah Kunle Hassan wanda ya gabatar da tambayoyi daga manema labarai a Muna kan halin da ake ciki, shi ma bai ji dadin shirin ciyarwar ba, wanda ya ce abincin bai wadatar ba.

Ya ce hukumar ta NAHCON ta yi hasashen cewa wannan matsala ta fi faruwa ne don haka ta ba da shawarar a shiga cikin lamarin, amma hukumomin Saudiyya da abin ya shafa sun dage cewa suna da babban dakin girki, da sanin makamar aiki da kuma wasu tsare-tsare guda uku na daban da za su gamsar da kowa.

Shugaban ya bayyana cewa tuni hukumarsa ta sanar da ma’aikatar aikin Hajji da Umrah ta Saudiyya kan halin da Nijeriya ke ciki dangane da tantuna da ciyarwa, inda ya ce an shirya za su hadu da daddare don duba halin da ake ciki a kasar tare da nemo mafita.

Tuni dai Alhazai suka ci gaba da gabatar da ibada da addu’o’i a filin Arfa.

Mahajjata
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Next Post
Da Buhari Ya Cire Tallafin Mai Da Tinubu Bai Zama Shugaban Kasa Ba —Garba Shehu

Da Buhari Ya Cire Tallafin Mai Da Tinubu Bai Zama Shugaban Kasa Ba —Garba Shehu

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.