ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mahajjata Sama Da Miliyan 2 Ne Za Su Yi Aikin Hajjin Bana

by Abubakar Abba
3 years ago
Mahajjata

Mahajjata sama da miliyan biyu daga sassa daban-daban na duniya ne da suka isa masarautar Saudiyya domin gudanar da aikin hajjin bana, sun yi dafifi a filin Arafah domin gudanar da ibada muhimmiya.

Alhazan dai tun daga wayewar garin ranar Talata suka fara tafiya Muna daga Makkah zuwa Arafah, Muzdalifah da komawa Muna, hakan ya nuna an fara aikin Hajjin.

  • Matawalle Bai Saci Kudin Jihar Zamfara Ba — Anas Kaura
  • Za Mu Kawar Da Matsalar Tsaro A Nijeriya -Nuhu Ribadu

Ana sa ran mahajjata za su kasance a filin Arafah a yau, daga bayan Sallar La’asar da La’asar zuwa faduwar rana, suna neman gafarar Allah, Rahma, Albarka, shiriya, aminci, kwanciyar hankali, ci gaba da sauran addu’o’i.

ADVERTISEMENT

Ana sa ran Malamai za su jagoranci mahajjatan Nijeriya wajen yin addu’o’in samun zaman lafiya, kwanciyar hankali, ci gaba da ci gaban al’ummar Nijeriya da kuma kasar ta shawo kan dukkan kalubalen da ta ke fuskanta ta fuskar tsaro da siyasa da tattalin arziki.

Bayan faduwar rana alhazai za su tashi zuwa Muzdalifah inda ake sa ran za su kwana kafin su koma Muna bayan an idar da sallar Asubah, domin jifan shaidan.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

A gefe guda kuwa, Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Nijeriya (NAHCON), ta nuna rashin gamsuwarta kan rashin isassun tantuna ga mahajjatan Nijeriya a Muna da Kamfanin Saudiyya ke da alhakin samarwa da isassun tantuna a Mashã’ir ga ‘yan Nijeriya.

Shugaban Hukumar Alhaji Zikrullah Kunle Hassan wanda ya gabatar da tambayoyi daga manema labarai a Muna kan halin da ake ciki, shi ma bai ji dadin shirin ciyarwar ba, wanda ya ce abincin bai wadatar ba.

Ya ce hukumar ta NAHCON ta yi hasashen cewa wannan matsala ta fi faruwa ne don haka ta ba da shawarar a shiga cikin lamarin, amma hukumomin Saudiyya da abin ya shafa sun dage cewa suna da babban dakin girki, da sanin makamar aiki da kuma wasu tsare-tsare guda uku na daban da za su gamsar da kowa.

Shugaban ya bayyana cewa tuni hukumarsa ta sanar da ma’aikatar aikin Hajji da Umrah ta Saudiyya kan halin da Nijeriya ke ciki dangane da tantuna da ciyarwa, inda ya ce an shirya za su hadu da daddare don duba halin da ake ciki a kasar tare da nemo mafita.

Tuni dai Alhazai suka ci gaba da gabatar da ibada da addu’o’i a filin Arfa.

Mahajjata
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Ɗaura Ɗamarar Magance Matsalolin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Matatar Ɗangote Ta Ƙaryata Iƙirarin Dillalan Man Fetur 

MASU ALAKA

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

July 8, 2026
Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi
Manyan Labarai

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

July 8, 2026
Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Waɗanda Aka Sace A Taraba
Manyan Labarai

Sojoji Da NDLEA Sun Kama Mutanen Da Ake Zargi Da Kai wa ’Yan Ta’adda Miyagun Ƙwayoyi A Katsina

July 8, 2026
Next Post
Da Buhari Ya Cire Tallafin Mai Da Tinubu Bai Zama Shugaban Kasa Ba —Garba Shehu

Da Buhari Ya Cire Tallafin Mai Da Tinubu Bai Zama Shugaban Kasa Ba —Garba Shehu

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

July 8, 2026
Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

July 8, 2026
Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

July 8, 2026
Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

July 8, 2026
Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

July 8, 2026
Damar Fita Daga Kangin Dalar Amurka Ta Sake Samuwa Ga Kasashen Afirka

Damar Fita Daga Kangin Dalar Amurka Ta Sake Samuwa Ga Kasashen Afirka

July 8, 2026
Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

July 8, 2026
NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

July 8, 2026
Xi Ya Yi Kira Da A Bunkasa Salon Zamanantarwa Na Sin Ta Hanyar Ingiza Kirkire-kirkiren Kimiyya Da Fasaha

Xi Ya Yi Kira Da A Bunkasa Salon Zamanantarwa Na Sin Ta Hanyar Ingiza Kirkire-kirkiren Kimiyya Da Fasaha

July 8, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Kwankwaso Ya Mayar wa Ali Modu Sheriff Martani, Ya Ce Peter Obi Na da Gagarumin Goyon Baya a Arewa

July 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.