ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mahajjata Sama Da Miliyan 2 Ne Za Su Yi Aikin Hajjin Bana

by Abubakar Abba
3 years ago
Mahajjata

Mahajjata sama da miliyan biyu daga sassa daban-daban na duniya ne da suka isa masarautar Saudiyya domin gudanar da aikin hajjin bana, sun yi dafifi a filin Arafah domin gudanar da ibada muhimmiya.

Alhazan dai tun daga wayewar garin ranar Talata suka fara tafiya Muna daga Makkah zuwa Arafah, Muzdalifah da komawa Muna, hakan ya nuna an fara aikin Hajjin.

  • Matawalle Bai Saci Kudin Jihar Zamfara Ba — Anas Kaura
  • Za Mu Kawar Da Matsalar Tsaro A Nijeriya -Nuhu Ribadu

Ana sa ran mahajjata za su kasance a filin Arafah a yau, daga bayan Sallar La’asar da La’asar zuwa faduwar rana, suna neman gafarar Allah, Rahma, Albarka, shiriya, aminci, kwanciyar hankali, ci gaba da sauran addu’o’i.

ADVERTISEMENT

Ana sa ran Malamai za su jagoranci mahajjatan Nijeriya wajen yin addu’o’in samun zaman lafiya, kwanciyar hankali, ci gaba da ci gaban al’ummar Nijeriya da kuma kasar ta shawo kan dukkan kalubalen da ta ke fuskanta ta fuskar tsaro da siyasa da tattalin arziki.

Bayan faduwar rana alhazai za su tashi zuwa Muzdalifah inda ake sa ran za su kwana kafin su koma Muna bayan an idar da sallar Asubah, domin jifan shaidan.

LABARAI MASU NASABA

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

A gefe guda kuwa, Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Nijeriya (NAHCON), ta nuna rashin gamsuwarta kan rashin isassun tantuna ga mahajjatan Nijeriya a Muna da Kamfanin Saudiyya ke da alhakin samarwa da isassun tantuna a Mashã’ir ga ‘yan Nijeriya.

Shugaban Hukumar Alhaji Zikrullah Kunle Hassan wanda ya gabatar da tambayoyi daga manema labarai a Muna kan halin da ake ciki, shi ma bai ji dadin shirin ciyarwar ba, wanda ya ce abincin bai wadatar ba.

Ya ce hukumar ta NAHCON ta yi hasashen cewa wannan matsala ta fi faruwa ne don haka ta ba da shawarar a shiga cikin lamarin, amma hukumomin Saudiyya da abin ya shafa sun dage cewa suna da babban dakin girki, da sanin makamar aiki da kuma wasu tsare-tsare guda uku na daban da za su gamsar da kowa.

Shugaban ya bayyana cewa tuni hukumarsa ta sanar da ma’aikatar aikin Hajji da Umrah ta Saudiyya kan halin da Nijeriya ke ciki dangane da tantuna da ciyarwa, inda ya ce an shirya za su hadu da daddare don duba halin da ake ciki a kasar tare da nemo mafita.

Tuni dai Alhazai suka ci gaba da gabatar da ibada da addu’o’i a filin Arfa.

Mahajjata
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilan Da Suka Sa Fannin Kiwo Ke Fuskantar Kalubale A Nijeriya —Gwamnatin Tarayya

MASU ALAKA

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar
Manyan Labarai

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle
Manyan Labarai

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Next Post
Da Buhari Ya Cire Tallafin Mai Da Tinubu Bai Zama Shugaban Kasa Ba —Garba Shehu

Da Buhari Ya Cire Tallafin Mai Da Tinubu Bai Zama Shugaban Kasa Ba —Garba Shehu

LABARAI MASU NASABA

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.