• English
  • Business News
Tuesday, October 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu Sanatoci Za Su Kalubalanci Nasarar Zaben Akpabio A Kotu

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Akpabio

Har zuwa yanzu dai tsugume ba ta kare ba kan shugabancin majalisar kasa ta 10 yayin da wasu fusatattun Sanatoci suka kammala shirye-shiryen garzayawa Kotu domin kalubalantar nasarar da Godswill Akpabio ya samu a matsayin shugaban majalisar dattawa.

Kamar yadda LEADERSHIP ta gano cewa, ‘Yan majalisar sun nuna rashin gamsuwarsu kan kuri’un da aka yi amfani da su a wajen zaben shugaban majalisar dattawan da zargin an tabka magudi a zaben.

  • Sanata Akpabio Ya Lashe Zaben Shugaban Majalisar Dattawa
  • An Rantsar Da Akpabio A Matsayin Shugaban Majalisar Dattawa Na 13

An kuma gano bayan zaben na majalisar dattawa ta 10, wasu Sanatoci na shirin yin tutsu ga jam’iyyar APC da barazanar ficewa daga cikinta.

Wata majiya daga majalisar ta shaida wa wakilinmu cewa Sanatoci 22 sun gama shirin sauya sheka zuwa wasu Jam’iyyun siyasa, ta yadda ‘yan adawa za su samu rinjaye a zauren majalisar.

Muddin wannan shirin ya tabbata, Jam’iyyun adawa za su samu mambobi 72 (Sanatoci) yayin da kuma APC za ta samu ragowar Sanatoci 37 kacal.

LABARAI MASU NASABA

Babu Rikici A Jam’iyyar APC A Nasarawa — Shugaban Jam’iyya

Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

Sai dai kuma tsohon mai tsawatarwa na majalisar dattawa, Sanata Orji Uzor Kalu, ya karyata zargin da wasu abokan aikinsa sanatoci suka yi, tare da cewa ba wasa Sanatocin suka yi ba a ranar 13 ga watan Yuni da suka zabi Akpabio a matsayin shugaban majalisar dattawa.

An gano Kalu wani faifayin bidiyo, ya ce, “A zahirin gaskiya zaben majalisar dattawa ya gudana bisa inganci. Sanata Akpabio ya ci zabensa. An yi bisa inganci kuma sahihin zabe.”

Kalu ya ce, ba a taba yin majalisa biyu ba, majalisa daya ce kuma sun riga sun kafata a ranar 13 ga watan Yuni tare da zaben shugaba da mataimaki.

To sai dai Sanatocin da suka zanta da wakilinmu sun yi watsi da ikirarin Kalu, suna masu hakikancewa kan ba za su bari sabon shugaban majalisar ya kammala wa’adinsa ba.

Wasu Sanatoci biyu daga arewa maso gabas masu ra’ayi irin fusatattun Sanatocin, sun ce, an malkwada zaben ne kawai domin a dakile takarar Sanata Abdul’aziz Yari.

Daya daga cikin Sanatocin wanda ya bukaci a sakaya sunansa ya ce, “Duk da an yi zabe har ma Akpabio ya samu nasara, amma akwai tulin ayoyin tambaya a kasa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Babu Rikici A Jam’iyyar APC A Nasarawa — Shugaban Jam’iyya
Siyasa

Babu Rikici A Jam’iyyar APC A Nasarawa — Shugaban Jam’iyya

October 21, 2025
Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu
Siyasa

Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

October 20, 2025
Tsohon Ɗan Majalisar Bayelsa Ya Shawarci Jonathan Ya Guji Neman Takara A 2027
Siyasa

Tsohon Ɗan Majalisar Bayelsa Ya Shawarci Jonathan Ya Guji Neman Takara A 2027

October 17, 2025
Next Post
Dole Ne Mace Ta Gaya Wa Mijinta Gaskiya Domin Ranar Hisabi – Matar Gwamnan Jigawa

Dole Ne Mace Ta Gaya Wa Mijinta Gaskiya Domin Ranar Hisabi - Matar Gwamnan Jigawa

LABARAI MASU NASABA

Me Aka Gano Kan Makomar Tattalin Arzikin Kasar Sin Daga Karuwar 5.2% Na Tattalin Arzikinta?

Me Aka Gano Kan Makomar Tattalin Arzikin Kasar Sin Daga Karuwar 5.2% Na Tattalin Arzikinta?

October 21, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Tabbatar Da Yusuf A Matsayin Sabon Shugaban NPC, Wasu 2 A Matsayin Kwamishinoni

October 21, 2025
Jirgin Kasa Mafi Saurin Gudu A Duniya Ya Fara Zirga-Zirgar Gwaji A Sin

Jirgin Kasa Mafi Saurin Gudu A Duniya Ya Fara Zirga-Zirgar Gwaji A Sin

October 21, 2025
Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu

Ma’aikatan Manyan Makarantu Na Kaduna Sun Dakatar Da Yajin Aiki Yayin Da Gwamna Sani Ya Amince Da Sabon Tsarin Albashi

October 21, 2025
Jami’an Kasashen Afrika Na Koyon Dabarar Yaki Da Talauci Ta Sin A Jihar Ningxia

Jami’an Kasashen Afrika Na Koyon Dabarar Yaki Da Talauci Ta Sin A Jihar Ningxia

October 21, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Wata Tankar Mai Ta Sake Fashewa A Neja

Da Ɗumi-ɗumi: Fashewar Tankar Man Fetur Ta Yi Ajalin Rayuka 30 A Neja

October 21, 2025
Sin Ta Bayar Da Tallafin Dala Miliyan 3.5 Ga Shirin Samar Da Abinci A Zambia

Sin Ta Bayar Da Tallafin Dala Miliyan 3.5 Ga Shirin Samar Da Abinci A Zambia

October 21, 2025
Babu Rikici A Jam’iyyar APC A Nasarawa — Shugaban Jam’iyya

Babu Rikici A Jam’iyyar APC A Nasarawa — Shugaban Jam’iyya

October 21, 2025
An Ɗage Shari’ar Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Zuwa 19 Ga Watan Nuwamba

An Ɗage Shari’ar Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Zuwa 19 Ga Watan Nuwamba

October 21, 2025
Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

October 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.