ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu Sanatoci Za Su Kalubalanci Nasarar Zaben Akpabio A Kotu

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Akpabio

Har zuwa yanzu dai tsugume ba ta kare ba kan shugabancin majalisar kasa ta 10 yayin da wasu fusatattun Sanatoci suka kammala shirye-shiryen garzayawa Kotu domin kalubalantar nasarar da Godswill Akpabio ya samu a matsayin shugaban majalisar dattawa.

Kamar yadda LEADERSHIP ta gano cewa, ‘Yan majalisar sun nuna rashin gamsuwarsu kan kuri’un da aka yi amfani da su a wajen zaben shugaban majalisar dattawan da zargin an tabka magudi a zaben.

  • Sanata Akpabio Ya Lashe Zaben Shugaban Majalisar Dattawa
  • An Rantsar Da Akpabio A Matsayin Shugaban Majalisar Dattawa Na 13

An kuma gano bayan zaben na majalisar dattawa ta 10, wasu Sanatoci na shirin yin tutsu ga jam’iyyar APC da barazanar ficewa daga cikinta.

ADVERTISEMENT

Wata majiya daga majalisar ta shaida wa wakilinmu cewa Sanatoci 22 sun gama shirin sauya sheka zuwa wasu Jam’iyyun siyasa, ta yadda ‘yan adawa za su samu rinjaye a zauren majalisar.

Muddin wannan shirin ya tabbata, Jam’iyyun adawa za su samu mambobi 72 (Sanatoci) yayin da kuma APC za ta samu ragowar Sanatoci 37 kacal.

LABARAI MASU NASABA

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna

Sai dai kuma tsohon mai tsawatarwa na majalisar dattawa, Sanata Orji Uzor Kalu, ya karyata zargin da wasu abokan aikinsa sanatoci suka yi, tare da cewa ba wasa Sanatocin suka yi ba a ranar 13 ga watan Yuni da suka zabi Akpabio a matsayin shugaban majalisar dattawa.

An gano Kalu wani faifayin bidiyo, ya ce, “A zahirin gaskiya zaben majalisar dattawa ya gudana bisa inganci. Sanata Akpabio ya ci zabensa. An yi bisa inganci kuma sahihin zabe.”

Kalu ya ce, ba a taba yin majalisa biyu ba, majalisa daya ce kuma sun riga sun kafata a ranar 13 ga watan Yuni tare da zaben shugaba da mataimaki.

To sai dai Sanatocin da suka zanta da wakilinmu sun yi watsi da ikirarin Kalu, suna masu hakikancewa kan ba za su bari sabon shugaban majalisar ya kammala wa’adinsa ba.

Wasu Sanatoci biyu daga arewa maso gabas masu ra’ayi irin fusatattun Sanatocin, sun ce, an malkwada zaben ne kawai domin a dakile takarar Sanata Abdul’aziz Yari.

Daya daga cikin Sanatocin wanda ya bukaci a sakaya sunansa ya ce, “Duk da an yi zabe har ma Akpabio ya samu nasara, amma akwai tulin ayoyin tambaya a kasa.

Akpabio
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora

MASU ALAKA

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu
Manyan Labarai

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna
Siyasa

Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna

September 9, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027
Siyasa

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Next Post
Dole Ne Mace Ta Gaya Wa Mijinta Gaskiya Domin Ranar Hisabi – Matar Gwamnan Jigawa

Dole Ne Mace Ta Gaya Wa Mijinta Gaskiya Domin Ranar Hisabi - Matar Gwamnan Jigawa

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar da Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC da NECO

Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Bai Wa Ɗalibai 100MB Na Data Kyauta Kullum

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

September 10, 2026
Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

September 10, 2026
Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026
Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.