• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NAFDAC Ta Fayyace Sakamakon Bincikenta Kan Taliyar Indomie

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
NAFDAC Ta Fayyace Sakamakon Bincikenta Kan Taliyar Indomie
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Darakta Janar ta Hukumar Kula da Abinci da Magunguna ta Kasa (NAFDAC), Farfesa Mojisola Adeyeye, ta bayyana cewa gwajin kimiyyar da hukumar ta gudanar ya tabbatar da cewa taliyar Indomie lafiyarta kalau babu wani hadari a tare da ita.

A lokacin da take jawabi ga manema labarai, Adeyeye ta jaddada ingancin lafiyar Indomie da ake samarwa a cikin gida Nijeriya. Ta tabbatar wa masu saye da sayar da kayayyakin abincin cewa, taliyar da aka janye ta “mai dandanon kaza ta musamman (Special Chicken Flabour)” a Taiwan da Malaysia ba ta tsallako cikin Nijeriya ba, don haka ba a sayar da ita ko’ina a kasuwannin Nijeriya.

  • Abin Da Ya Kamata A Sani Game Da Barkewar Cutar Diptheria A Abuja
  • Ina Son Kara Aure, Ko Me Yake Kawo Matsaloli Tsakanin Kishiyoyi Da Yadda Za A Magance?

A cewar shugabar ta NAFDAC, “An gwada jimillar samfura guda 114 na taliyar da abubuwan da suka hada da sinadarai daban-daban na ingancin abinci. Mun samu samfurori 58 daga masana’antu daban-daban, samfurori 24 daga kasuwannin Legas, samfurori 16 daga Abuja, da kuma samfurori 16 daga Kano. An yi amfani da hanyoyi guda biyu don gwada samfurori daban-daban da aka tattara, su ne: dabarar nazari da ake amfani da ita don rarrabewa da gano abubuwan da ke tattare da sinadarai, da kuma dabarar nazarin da ake gano abubuwan sinadarai ta hanyar tantancewa.”

Da take bayani kan jinkirin da aka samu wajen fitar da sakamakon binciken, Adeyeye ta bayyana cewa, hakan ta faru ne saboda wasu kayan aiki da fasahar zamanin da aka yi amfani da su dole sai da aka shigo da su cikin kasar nan daga waje, sannan hukumar ta NAFDAC ta natsu ce ta yi aikin a kimiyance.

Domin nuna gamsuwa da kuma amincewarta da sakamakon gwajin da aka yi, shugabar ta NAFDAC ta cinye taliyar indomie da aka girka aka zuba mata a lokacin taron, inda abokan aikinta suka bukaci su ma ta raba musu ko da taba-ka-lashe.

Manajan Sadarwa da Shirya Bukukuwa na Kamfanin Dufil Prima Foods Plc, Temitope Ashiwaju ya bayyana kudurin kamfanin na kiyaye ka’idojin tabbatar da inganci na kasa da kuma duniya tare da tallafa wa bunkasa tattalin arzikin cikin gida.

Da yake karin haske daga ofishin Dufil Prima Foods da ke Legas, Ashiwaju ya ce, “Ana samar da nau’ikan taliyar Indomie ne a Nijeriya kuma an shafe akalla shekaru talatin ana sarrafa taliyar a kasar. Dupil Prima ya kara fadada ayyukan da yake yi a cikin gida wanda hakan zai bunkasa yawan kayan da yake sarrafawa da daukar ma’aikata domin cimma bukatun kasuwa da zarce ka’idojin da aka gindaya na inganci a gida da waje.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BincikeIndomieNAFDAC
ShareTweetSendShare
Previous Post

Bidiyon Dala: Kotu Ta Dakatar Da Gwamnatin Kano Da ‘Ƴansanda Da DSS Kan Kama Ganduje

Next Post

An Maka Shi Gaban Kotu Bisa Satar Karafan Naira Miliyan 5

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

2 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

3 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

4 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

8 hours ago
NAFDAC
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

9 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

10 hours ago
Next Post
An Daure Matashi Shekara 1 Kan Satar Janareta A Abuja

An Maka Shi Gaban Kotu Bisa Satar Karafan Naira Miliyan 5

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.