• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Kamata A Sani Game Da Barkewar Cutar Diptheria A Abuja

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
in Labarai
0
Abin Da Ya Kamata A Sani Game Da Barkewar Cutar Diptheria A Abuja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An samu barkewar cutar Diphtheria da ta kashe yaro mai shekara hudu a garin Dei-Dei da ke babban birnin tarayya Abuja, wanda hakan ya sa hankalin mutane ya tashi musamman ma la’akari da yadda kwayar cutar take yaduwa tsakanin mutane.

Hukumar Babban Birnin Tarayya ta tabbatar da yaduwar cutar bayan da aka yi gwajin mutane takwas a dakin gwajin da ke Gaduwa da hukumar hana yaduwar cutar ta gudanar.

  • Bukatar Dakatar Da Kara Kudin Wutar Lantarki A Nijeriya
  • Kamfanin Meta Mamallakin Facebook Ya Yi Wa Twitter Kishiya

Diphtheria cuta ce da take farawa da zazzabi wanda yake saurin yaduwa ta hanyar tari da kuma hamma, kamar yadda hukumar lafiya ta duniya ta tabbatar.

 “Idan abin ya ta’azzara, kwayar cutar tana iya yin guba da take sa wani farin abu a bayan makogwaro wanda ke toshe hanyoyin da iska za ta shiga, abin da zai samar da matsala wajen shakar iska ko hadiya, da haka ne sai a fara tari mai zafi. Akwai wani sashe na wuya na iya kumburi saboda kwayar cutar ta yi sanadiyar ta kama wurin.

 “A hankali gubar na iya haduwa da jini wanda hakan na iya samar da matsala da lalata naman zuciya da za su iya shafar jijiya, koda da saboda karancin kwayar halitta ta jini da ke sa rauni saurin warkewa”.

Labarai Masu Nasaba

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna

Jihohi 10 Sun Kinkimo Bashin Naira Biliyan 417 Duk Da Karin Samun Kudaden Shiga

Cutar ana yin maganinta ta hanyar amfani da magani da kuma na yin allurar Diphtheria.

Domin kauce wa kamuwa da cutar, babban sakataren kula da lafiya na Abuja, Yahaya Batsa, ya yi kira da mutane su je su yi allurar rigakafi, su yi nesa da shiga cikin jama’a da kuma daina zama wuraren da babu tsafta. Ya ba da shawarar a yi wa yara allurar rigakafi kamar yadda ya dace sau uku na allurar Pentabalent.

Hukumar lafiya ta duniya ta yi bayanin cewar a tabbatar da yin allurar rigakafin cutar Diphtheria ga yara da samari, saboda gujewar barkewar cutar.

Akwai allurar rigakafi ta da take bukatar ba kamar yadda ake yi ba sau uku, wanda hakan zai sa a samu damar yi wa yara da yawa allurar rigakafin da ya kamata saboda kariya daga kamuwa da cututtuka kamar su Diphtheria.

Asusun kula da yara na Majalisar Dinkin Duniya yana sa ran hukumar lafiya ta duniya za ta assasa yin allurar rigakafi nan da wata uku masu zuwa ko rubi’in shekarar 2023.

Alkalumma da aka samu daga hukumar lafiya ta duniya sun nuna cewa an samu wadanda suka kamu da cutar Diptheria 557 a Nijeriya daga watan Afrilu na 2023, ya shafi jihohi 21 daga cikin 36 tare da babban birnin tarayya.

An sanar da cibiyar hana yaduwar cututtuka da maganisu ta kasa a watan Disamba 2022, dangane da barkewar cutar Diphtheria a jihohin Kano da Legas.

Daga ranar 14 ga watan Mayu zuwa 9 ga Afrilu 2022, an samu wadanda ake kyautata sun kamu da cutar guda 1439, amma daga karshe an samu 557 ko kashi 39 da aka tabbatar da sun kamu da mutuwar mutum 73 daga cikin wadanda suka kamu da cutar.

A Nijeriya an fara samun labarin barkewar cutar Diphtheria a shekarar 2011 da ta shafi wasu wurare a kauyukan Jihar Borno, sashen Arewa maso gabas.

Alamun kamuwa da cutar sun hada da zazzabi, majina ta rika zuba, ciwon mashako, tari, idanu su yi ja, kumburin wuya, sai samun matsalar yin numfashi. Cutar Diphtheria tana saurin yaduwa ta hanyar cudanya da wanda ya kamu da ita.

Domin tabbatar da an kauce wa yiyuwar kamuwa da cutar, an yi kira da mazauna babban burnin tarayya su tabbatar da an yi wa ‘ya’yansu alluran rigakafi sau uku na Pentabalent wato yadda aka amince da sharuddan alluran rigakafi na kasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbujaCutaDiptheria
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Bukaci Japan Da Kada Ta Yi Yunkurin Amfani Da Rahoton IAEA A Matsayin Izinin Zubar Da Dagwalon Ruwan Nukiliya A Cikin Teku

Next Post

An Bude Dandalin Hadin Gwiwa Da Raya Kirkire-kirkire Na Sin Da Afirka

Related

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna
Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna

45 minutes ago
Jihohi 10 Sun Kinkimo Bashin Naira Biliyan 417 Duk Da Karin Samun Kudaden Shiga
Labarai

Jihohi 10 Sun Kinkimo Bashin Naira Biliyan 417 Duk Da Karin Samun Kudaden Shiga

1 hour ago
Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Shirin Ciyar Da Ɗalibai A Makarantun Zamfara
Labarai

Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Shirin Ciyar Da Ɗalibai A Makarantun Zamfara

1 hour ago
Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda ÆŠumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista
Manyan Labarai

Shugabannin Jam’iyyar ADC Na Jihohi 36 Da Abuja Sun Bayyana Goyon Bayansu Ga David Mark

2 hours ago
Gwamnan Zamfara Ya Raba Buhunan Taki 59,205 Ga Manoman Jihar
Labarai

Gwamnan Zamfara Ya Raba Buhunan Taki 59,205 Ga Manoman Jihar

2 hours ago
Matatun Man Fetur Na Nijeriya Ba Za Su Ci Gaba Da Aiki Yadda Ya Kamata Ba – Dangote
Manyan Labarai

Matatun Man Fetur Na Nijeriya Ba Za Su Ci Gaba Da Aiki Yadda Ya Kamata Ba – Dangote

3 hours ago
Next Post
An Bude Dandalin Hadin Gwiwa Da Raya Kirkire-kirkire Na Sin Da Afirka

An Bude Dandalin Hadin Gwiwa Da Raya Kirkire-kirkire Na Sin Da Afirka

LABARAI MASU NASABA

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna

July 11, 2025
Jihohi 10 Sun Kinkimo Bashin Naira Biliyan 417 Duk Da Karin Samun Kudaden Shiga

Jihohi 10 Sun Kinkimo Bashin Naira Biliyan 417 Duk Da Karin Samun Kudaden Shiga

July 11, 2025
Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Shirin Ciyar Da Ɗalibai A Makarantun Zamfara

Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Shirin Ciyar Da Ɗalibai A Makarantun Zamfara

July 11, 2025
Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda ÆŠumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

Shugabannin Jam’iyyar ADC Na Jihohi 36 Da Abuja Sun Bayyana Goyon Bayansu Ga David Mark

July 11, 2025
Gwamnan Zamfara Ya Raba Buhunan Taki 59,205 Ga Manoman Jihar

Gwamnan Zamfara Ya Raba Buhunan Taki 59,205 Ga Manoman Jihar

July 11, 2025
Matatun Man Fetur Na Nijeriya Ba Za Su Ci Gaba Da Aiki Yadda Ya Kamata Ba – Dangote

Matatun Man Fetur Na Nijeriya Ba Za Su Ci Gaba Da Aiki Yadda Ya Kamata Ba – Dangote

July 11, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

‘Yan Bindiga Sun Kai Wa ‘Yansanda Hari Tare Da Kashe Wani Mutum Da Raunata Wani A Nasarawa

July 11, 2025
Goron Sallah

GORON JUMA’A

July 11, 2025
An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa

An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa

July 11, 2025
Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 

Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.