• English
  • Business News
Wednesday, July 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NAFDAC Ta Fayyace Sakamakon Bincikenta Kan Taliyar Indomie

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
NAFDAC Ta Fayyace Sakamakon Bincikenta Kan Taliyar Indomie
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

Darakta Janar ta Hukumar Kula da Abinci da Magunguna ta Kasa (NAFDAC), Farfesa Mojisola Adeyeye, ta bayyana cewa gwajin kimiyyar da hukumar ta gudanar ya tabbatar da cewa taliyar Indomie lafiyarta kalau babu wani hadari a tare da ita.

A lokacin da take jawabi ga manema labarai, Adeyeye ta jaddada ingancin lafiyar Indomie da ake samarwa a cikin gida Nijeriya. Ta tabbatar wa masu saye da sayar da kayayyakin abincin cewa, taliyar da aka janye ta “mai dandanon kaza ta musamman (Special Chicken Flabour)” a Taiwan da Malaysia ba ta tsallako cikin Nijeriya ba, don haka ba a sayar da ita ko’ina a kasuwannin Nijeriya.

  • Abin Da Ya Kamata A Sani Game Da Barkewar Cutar Diptheria A Abuja
  • Ina Son Kara Aure, Ko Me Yake Kawo Matsaloli Tsakanin Kishiyoyi Da Yadda Za A Magance?

A cewar shugabar ta NAFDAC, “An gwada jimillar samfura guda 114 na taliyar da abubuwan da suka hada da sinadarai daban-daban na ingancin abinci. Mun samu samfurori 58 daga masana’antu daban-daban, samfurori 24 daga kasuwannin Legas, samfurori 16 daga Abuja, da kuma samfurori 16 daga Kano. An yi amfani da hanyoyi guda biyu don gwada samfurori daban-daban da aka tattara, su ne: dabarar nazari da ake amfani da ita don rarrabewa da gano abubuwan da ke tattare da sinadarai, da kuma dabarar nazarin da ake gano abubuwan sinadarai ta hanyar tantancewa.”

Da take bayani kan jinkirin da aka samu wajen fitar da sakamakon binciken, Adeyeye ta bayyana cewa, hakan ta faru ne saboda wasu kayan aiki da fasahar zamanin da aka yi amfani da su dole sai da aka shigo da su cikin kasar nan daga waje, sannan hukumar ta NAFDAC ta natsu ce ta yi aikin a kimiyance.

Domin nuna gamsuwa da kuma amincewarta da sakamakon gwajin da aka yi, shugabar ta NAFDAC ta cinye taliyar indomie da aka girka aka zuba mata a lokacin taron, inda abokan aikinta suka bukaci su ma ta raba musu ko da taba-ka-lashe.

Manajan Sadarwa da Shirya Bukukuwa na Kamfanin Dufil Prima Foods Plc, Temitope Ashiwaju ya bayyana kudurin kamfanin na kiyaye ka’idojin tabbatar da inganci na kasa da kuma duniya tare da tallafa wa bunkasa tattalin arzikin cikin gida.

Da yake karin haske daga ofishin Dufil Prima Foods da ke Legas, Ashiwaju ya ce, “Ana samar da nau’ikan taliyar Indomie ne a Nijeriya kuma an shafe akalla shekaru talatin ana sarrafa taliyar a kasar. Dupil Prima ya kara fadada ayyukan da yake yi a cikin gida wanda hakan zai bunkasa yawan kayan da yake sarrafawa da daukar ma’aikata domin cimma bukatun kasuwa da zarce ka’idojin da aka gindaya na inganci a gida da waje.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BincikeIndomieNAFDAC
ShareTweetSendShare
Previous Post

Bidiyon Dala: Kotu Ta Dakatar Da Gwamnatin Kano Da ‘Ƴansanda Da DSS Kan Kama Ganduje

Next Post

An Maka Shi Gaban Kotu Bisa Satar Karafan Naira Miliyan 5

Related

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa
Labarai

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

2 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

3 hours ago
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma
Labarai

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

4 hours ago
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100
Labarai

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

5 hours ago
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano
Manyan Labarai

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

6 hours ago
Ba Gaskiya Ba Ne: Ɓarayi Ba Su Sace Ɗan Uwan Gwamnan Zamfara Ba
Labarai

Ba Gaskiya Ba Ne: Ɓarayi Ba Su Sace Ɗan Uwan Gwamnan Zamfara Ba

7 hours ago
Next Post
An Daure Matashi Shekara 1 Kan Satar Janareta A Abuja

An Maka Shi Gaban Kotu Bisa Satar Karafan Naira Miliyan 5

LABARAI MASU NASABA

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

July 1, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

July 1, 2025
An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

July 1, 2025
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

July 1, 2025
Kayan Aro Baya Rufe Katara

Kayan Aro Baya Rufe Katara

July 1, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

July 1, 2025
Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

July 1, 2025
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

July 1, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

July 1, 2025
An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

July 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.