• English
  • Business News
Wednesday, October 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sarkin Kabilar Zulu Ya Musanta Batun Ba Shi Guba

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Zulu

Sarkin Zulu na Afirka ta Kudu, Misuzulu kaZwelithini, ya musanta zargin da ake yi cewa watakila an ba shi guba, yana mai cewa yana cikin koshin lafiya.

Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da ake takaddama bayan da firaministansa na gargajiya ya fada a karshen mako cewa sarkin na jinya a Eswatini bisa zargin ya ci guba.

  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 4 Da Ceto Mutum 24 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Zamfara
  • ‘Muhallin Mutum 43,000 Aka Cunkusa Alhazan Nijeriya 95,000 A Mina’

Cif Mangosuthu Buthelezi ya ce sarkin na kwance a asibiti sakamakon mutuwar daya daga cikin manyan mashawartansa, wanda kuma ake zargin shi ma guba ce ta kashe shi, amma mai magana da yawun sarkin ya musanta hakan inda ya ce yana cikin koshin lafiya.

Cikin faifan bidiyon da aka raba wa manema labarai na Afirka ta Kudu, sarkin ya ce an tsara zai dinga zuwa duba lafiyarsa akai-akai, wanda ya yanke shawarar yi a Eswatini.

“Ni ban ci wata guba ba, ina cikin koshin lafiyata 100 bisa 100.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Kwara

Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

“Ina cikin farin ciki saboda ina da koshin lafiya, babu wata guba da na ci. Don haka mutane, al’ummar Zulu, da dangina su tunatar da jama’a cewa kada a saurari duk abin da mutane ke fadi, ”in ji shi.

An kuma ambato Sarki Misuzulu yana shaida wa kamfanin dillancin labarai na AFP ta wayar tarho daga Eswatini cewa “yana cikin koshin lafiya sosai”.

Sarkin mai shekara 48 ya hau karagar mulki a shekarar da ta gabata bayan rasuwar mahaifinsa Sarki Goodwill Zwelithini a wani zazzafan rikici da ya barke kan gadon sarautar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Kwara

October 15, 2025
Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima
Manyan Labarai

Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

October 15, 2025
Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 
Labarai

Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

October 14, 2025
Next Post
Sama Da Motoci Miliyan 3 Masu Amfani Da Sabon Makamashi Aka Yi Wa Rejista A Rabin Farkon Bana A Kasar Sin 

Sama Da Motoci Miliyan 3 Masu Amfani Da Sabon Makamashi Aka Yi Wa Rejista A Rabin Farkon Bana A Kasar Sin 

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Kwara

October 15, 2025
Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

October 15, 2025
Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

October 14, 2025
Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

October 14, 2025
Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

October 14, 2025
Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

October 14, 2025
Kotu

Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta

October 14, 2025
Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

October 14, 2025
Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya

Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya

October 14, 2025
Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo

Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo

October 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.