ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
11 months ago
Sheikh Dahiru Bauchi

Gidauniyar Sheikh Dahiru Usman Bauchi ta tura ɗalibai 117 ƙasar Algeria domin yin karatu a ɓangarori daban-daban ciki har da ilimin likitanci, injiniyanci da sauran muhimman ɓangarori na ilimi.

 

Daraktan sashin ilimi na gidauniyar, Gwani Aliyu Dahiru Bauchi, ya yi bayanin cewa dukkanin ɗaliban da suka samu guraben karatun su 140 ne, inda a yanzu haka 117 suka kammala shirin su na tafiya yayin da sauran 23 kuma za su tafi daga baya bayan kammala cike sauran ƙa’idoji.

ADVERTISEMENT
  • Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo
  • Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

Ya ce ɗaliban sun fito ne daga jihohi sama da bakwai da suka haɗa da Bauchi, Gombe, Yobe, Kaduna, Taraba, Adamawa da sauran jihohin da suke Nijeriya.

 

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Sayyidi Aliyu ya shaida hakan ne yayin jawabin bankwana da wayar da kan ɗaliban da suka samu gurbin karatun zuwa ƙasar Algeria na shekarar 2025, da ya gudana a cibiyar Sheikh Dahiru da ke Bauchi a ranar Litinin 13 ga watan Oktoba.

 

Ya ce an ɗauki tsawon lokaci ana wayar da kan ɗaliban na tsawon shekara guda kan yadda za su kyautata rayuwarsu a can ƙasar da kuma samun ilimin da ake tsammani a garesu ba tare da matsaloli ba tare da koyar musu harsunan Farsanci da Larabci domin sauƙaƙa musu fara rayuwa a ƙasar Algeria.

 

Ya yaba wa Gwamnan jihar Bauchi Bala Muhammad bisa biyan kuɗin jirgi wa dukkani ɗaliban jihar su 50 daga cikin waɗanda za su tafi ƙasar neman ilimi.

 

Kazalika, ya kuma gode wa gwamnan bisa roƙa musu da ya yi na cewar a bai wa ‘yan Nijeriya damar koyon ilimin likitanci, “A lokacin da tawaga daga Algeriya suka zo jihar Bauchi, gwamna Bala Muhammad ya yi roƙo na cewar a ake amincewa ɗaliban Nijeriya samun ilimin likitanci a ƙasar Algeriya, wanda a da baya ba su bai wa kowa damar samun wannan sai ‘yan ƙasar amma suka amince, lallai wannan abun yabo ne sosai,” ya shaida.

 

Ya ce bayan kuɗin ticket komai na hidimar karatun kyauta ne wanda gwamnatin ƙasar Algeria ta ɗauki nauyi ga waɗanda suka samu nasarar samun guraben, wanda suke da damar yin karatu daga digiri har digiri na biyu (masters), sai ya yi bayanin cewa suna kan ƙoƙarin neman damar samar wa ɗalibai guraren digirin digirgir (PhD).

 

Ya ƙara da cewa wannan shi ne karo na biyu domin a farko gidauniya ta tura ɗalibai 66 zuwa ƙasar Algeriya wanda zuwa yanzu wasu ma har sun kammala digiri a fannonin ilimi daban-daban.

 

Jagoran ya nuna kwarin guiwar cewa idan ɗaliban suka kammala karatun nasu, ƙasar Nijeriya za ta moresu matuƙa gaya. Ya hori ɗaliban da suka samu tallafin karatun da su maida hankali wajen yin abun da ya kamata domin samun ilimi mai inganci tare da nemansu da su zama jakadu na kwarai ga Nigeria.

 

Kazalika, ya jinjina wa Sheikh Dahiru Usman Bauchi bisa gayar gudunmawar da yake bayarwa wajen kyautata harkokin ilimin addini da na zamani, ya ce, bayan gudunmawar da yake bayarwa wajen samar da mahaddata yanzu haka ana samun masu karatu a ɓangarori daban-daban na ilimi sakamakon ƙoƙarinsa.

 

Sadiyya Auwal wacce ta samu gurbin karatu domin karanta ilimin likitanci, ta gode wa Sheikh Dahiru da daraktan ilimin gidauniyar bisa kokarinsu da ya kai su ga samun damar karatun tare da tabbatar da cewa za ta maida hankali domin samun nasarar abun da za ta je yi can ƙasar Algeria.

 

Shi ma Mukhtar Ahmed wanda ya samu gurbin ƙaratun ilimin kimiyyar na’ura mai ƙwaƙwalwa (Computer Science) ya nuna godiya wa gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi kan damar da ta samar musu, ya ce tsawon shekara ana faɗi tashi don nema musu tafiya karatun.

 

Ya bada tabbacin maida hankali domin samun ilimi mai inganci tare da dawowa Nijeriya domin bayar da nasa gudunmawar.

Sheikh Dahiru Bauchi
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ‘Yansanda Sun Cafke Tsoho Mai Shekara 70 Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 8 Fyaɗe A Bauchi
Sheikh Dahiru Bauchi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Next Post
Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.