ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
8 months ago
Sheikh Dahiru Bauchi

Gidauniyar Sheikh Dahiru Usman Bauchi ta tura ɗalibai 117 ƙasar Algeria domin yin karatu a ɓangarori daban-daban ciki har da ilimin likitanci, injiniyanci da sauran muhimman ɓangarori na ilimi.

 

Daraktan sashin ilimi na gidauniyar, Gwani Aliyu Dahiru Bauchi, ya yi bayanin cewa dukkanin ɗaliban da suka samu guraben karatun su 140 ne, inda a yanzu haka 117 suka kammala shirin su na tafiya yayin da sauran 23 kuma za su tafi daga baya bayan kammala cike sauran ƙa’idoji.

ADVERTISEMENT
  • Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo
  • Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

Ya ce ɗaliban sun fito ne daga jihohi sama da bakwai da suka haɗa da Bauchi, Gombe, Yobe, Kaduna, Taraba, Adamawa da sauran jihohin da suke Nijeriya.

 

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Sayyidi Aliyu ya shaida hakan ne yayin jawabin bankwana da wayar da kan ɗaliban da suka samu gurbin karatun zuwa ƙasar Algeria na shekarar 2025, da ya gudana a cibiyar Sheikh Dahiru da ke Bauchi a ranar Litinin 13 ga watan Oktoba.

 

Ya ce an ɗauki tsawon lokaci ana wayar da kan ɗaliban na tsawon shekara guda kan yadda za su kyautata rayuwarsu a can ƙasar da kuma samun ilimin da ake tsammani a garesu ba tare da matsaloli ba tare da koyar musu harsunan Farsanci da Larabci domin sauƙaƙa musu fara rayuwa a ƙasar Algeria.

 

Ya yaba wa Gwamnan jihar Bauchi Bala Muhammad bisa biyan kuɗin jirgi wa dukkani ɗaliban jihar su 50 daga cikin waɗanda za su tafi ƙasar neman ilimi.

 

Kazalika, ya kuma gode wa gwamnan bisa roƙa musu da ya yi na cewar a bai wa ‘yan Nijeriya damar koyon ilimin likitanci, “A lokacin da tawaga daga Algeriya suka zo jihar Bauchi, gwamna Bala Muhammad ya yi roƙo na cewar a ake amincewa ɗaliban Nijeriya samun ilimin likitanci a ƙasar Algeriya, wanda a da baya ba su bai wa kowa damar samun wannan sai ‘yan ƙasar amma suka amince, lallai wannan abun yabo ne sosai,” ya shaida.

 

Ya ce bayan kuɗin ticket komai na hidimar karatun kyauta ne wanda gwamnatin ƙasar Algeria ta ɗauki nauyi ga waɗanda suka samu nasarar samun guraben, wanda suke da damar yin karatu daga digiri har digiri na biyu (masters), sai ya yi bayanin cewa suna kan ƙoƙarin neman damar samar wa ɗalibai guraren digirin digirgir (PhD).

 

Ya ƙara da cewa wannan shi ne karo na biyu domin a farko gidauniya ta tura ɗalibai 66 zuwa ƙasar Algeriya wanda zuwa yanzu wasu ma har sun kammala digiri a fannonin ilimi daban-daban.

 

Jagoran ya nuna kwarin guiwar cewa idan ɗaliban suka kammala karatun nasu, ƙasar Nijeriya za ta moresu matuƙa gaya. Ya hori ɗaliban da suka samu tallafin karatun da su maida hankali wajen yin abun da ya kamata domin samun ilimi mai inganci tare da nemansu da su zama jakadu na kwarai ga Nigeria.

 

Kazalika, ya jinjina wa Sheikh Dahiru Usman Bauchi bisa gayar gudunmawar da yake bayarwa wajen kyautata harkokin ilimin addini da na zamani, ya ce, bayan gudunmawar da yake bayarwa wajen samar da mahaddata yanzu haka ana samun masu karatu a ɓangarori daban-daban na ilimi sakamakon ƙoƙarinsa.

 

Sadiyya Auwal wacce ta samu gurbin karatu domin karanta ilimin likitanci, ta gode wa Sheikh Dahiru da daraktan ilimin gidauniyar bisa kokarinsu da ya kai su ga samun damar karatun tare da tabbatar da cewa za ta maida hankali domin samun nasarar abun da za ta je yi can ƙasar Algeria.

 

Shi ma Mukhtar Ahmed wanda ya samu gurbin ƙaratun ilimin kimiyyar na’ura mai ƙwaƙwalwa (Computer Science) ya nuna godiya wa gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi kan damar da ta samar musu, ya ce tsawon shekara ana faɗi tashi don nema musu tafiya karatun.

 

Ya bada tabbacin maida hankali domin samun ilimi mai inganci tare da dawowa Nijeriya domin bayar da nasa gudunmawar.

Sheikh Dahiru Bauchi
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba
Sheikh Dahiru Bauchi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • Sulaiman
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Next Post
Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.