ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

by CGTN Hausa and Sulaiman
8 months ago
Mace

A jiya Litinin shugaban kasar Sin ya kaddamar da taron koli na mata na duniya a birnin Beijing, inda ya gabatar da jawabi tare da shawarwari 4 na kasar Sin kan inganta ci gaban harkokin mata a duniya. Jawabin na shugaba Xi ya ja hankalin mahalarta da ma jama’ar duniya inda suke ganin ya aza wani sabon tubalin hadin gwiwa tsakanin kasa da kasa a bangaren raya harkokin mata.

Wannan taro a ganina, ya zo a daidai lokacin da ake bukatarsa. Bayan shekaru 30 da cimma yarjejeniyar Beijing da ta zama jigo wajen raya harkokin mata, an samu sabbin sauye-sauye a duniya wadanda ke bukatar sabbin dabaru. Kuma haduwar da aka yi a yanzu, zai kara ba mata a duniya kwarin gwiwa da bayyana musu cewa, suna da makoma mai haske. Baya ga haka, zuwan mahalartan kasar Sin zai nuna musu irin ci gaban da Sin ta samu a fannin domin su dauki darasi.

Kasar Sin ta bayar da gagarumar gudunmawa ga raya harkokin mata a duniya, inda take zurfafa musaya da hadin gwiwa a fannonin da suka shafi mata domin taimakawa mata a kasashe masu tasowa inganta rayuwarsu da cimma burikansu. Misali, ta horar da mata sama da 200,000 daga kasashe da yankuna sama da 180, baya ga shirye-shiryen horar da mata sama da 100 da ta aiwatar a kasashe masu tasowa.

ADVERTISEMENT

Idan muka dawo cikin gida, za mu fahimci furucin shugaba Xi cewa, “kowacce mace tauraruwa ce a sabon tafarkin zamanantar da kasar Sin” domin kasar tana iyakar kokarinta wajen tabbatar da daidaiton jinsi cikin dukkan manufofinta na kasa da ba mata damar taka rawa daidai da maza. Sin na daya daga cikin kasashen duniya dake da adadin mai yawa na mata ma’aikata, inda suka dauki kaso 40 cikin 100. Mata Sinawa, suna ci gaba da taka rawar gani a dukkan bangarori na rayuwa. Ni ganau ce na yadda mata a yankunan karkara suka tashi tsaye wajen marawa gwamnati baya a yakin da ta yi da talauci da kuma ci gaba da ake yi na ganin hannun agogo bai koma baya ba. Wani babban batu shi ne, yadda ake aiwatarwa da gyara dokoki domin tabbatar da mata sun samu damarmaki iri daya da takwarorinsu maza, daga bangaren ilimi zuwa na mallakar kadarori da gidan aure da zamantakewa da sauransu. Haka zalika a bangaren siyasa, inda ake da mata masu jagorantar hukumomi da kwamitocin siyasa a kasar.

Shawarwarin shugaba Xi Jinping, abu ne da kasa da kasa za su iya aiwatarwa domin an yi a Sin kuma kwalliya ta biya kudin sabulu. Za mu iya cewa, wannan taro ya sake samar wa duniya karin kafa ta hadin gwiwa domin tattaunawa da hada karfi da karfe wajen gaggauta samar da ci gaba mai ma’ana a fagen kare hakkokin mata da goya musu baya wajen taka rawar gani a harkokin da suka shafi bunkasa tattalin arziki da zamantakewa da ma bayar da gudunmawa ga ci gaban duniya. (Fa’iza Mustapha)

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Mace
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
Mace
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
Kotu

Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.