• English
  • Business News
Thursday, October 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Rade-Radin Bullar Cutar ‘Diphtheria’ A Garin Potiskum Na Jihar Yobe

by Muhammad Maitela
2 years ago
Diphtheria

Wasu majiyoyi a garin Potiskum sun tabbatar da bullar sabuwar cutar nan ta ‘Diphtheria’ a garin, inda a halin yanzu an samu mutuwar yara da dama yayin da aka kwantar da wasu a cibiyoyin kebe majinyata a sibitin garin.

Dr. Umar Chiroma, shi ne mukaddashin babban sakataren hukumar kula da lafiya a matakin farko na jihar Yobe, ya shaida wa wakilinmu cewa, “Lokacin da muka samu rahoton bullar cutar a garin Potiskum a karshen mako, nan take muka hada tawaga zuwa wuraren da abin ya shafa don wayar da kan jama’a tare da dakile yaduwarta cikin al’umma, ”

  • Yanzu-yanzu: Hon. Buba Mashio Ya Zama Sabon Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Yobe
  • ‘Yansanda Sun Cafke Wasu Yara 2 Da Mahaifinsu Kan Kashe Wani Mutum A Yobe

“Duk da a yanzu ba za mu iya bayyana shi a matsayin Diphtheria ba har sai mun dauki samfurin kwayar cutar mun bincika daga nan za mu iya sanar da abin da ake ciki.”

‘’Wasu daga cikin majinyatan sun haura shekaru 30, wasu 14 yayin da wasu kuma ‘yan shekara 12 zuwa 8 ne. Sannan wani abin takaici shi ne, wasu daga cikin majinyata suna daga cikin wadanda suka bijirewa allurar riga-kafi, wanda hakan ya sa ya fi shafar yaran da ba su yi riga-kafin ba.” In ji shi.

Dr. Chiroma ya kara da cewa, ‘’Wasu daga cikin majinyatan sun warke, don haka ba za mu iya tabbatar da cewa cutar Diphtheria ce har sai idan binciken masana ya gano ita ce, ”

LABARAI MASU NASABA

Da Ɗumi-ɗumi: Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ya Ƙara Raguwa Zuwa Kashi 18.02%

2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa

“Da safiyar yau Talata na samu labarin bullar cutar daga daraktan da yake kula da wannan shiyya, saboda haka har yanzu ba mu sami adadin mace-macen a hukumance ba.” Cewar Dr. Chiroma.

Unguwanin da abin ya fi kamari sun hada da unguwar Tandari, Misau Road, Sabuwar Sakateriya, Arikime, Ramin Kasa, Boriya, Yuganda da Texaco quarters.

Wata majiya daga cibiyar kebance majinyata na asibitin kwararru da ke Potiskum ta bayyana cewa suna fuskantar karancin magungunan da za su shawo kan lamarin.

Wata majiya ta shaidawa wakilinmu cewa sama da mutum 46 ne aka kwantar a asibitin, inda yara 20 suka mutu a gida tare da karin wasu 4 da suka mutu a asibitin.

Abdullahi Muhammad, daga garin na Potiskum ya ce ‘’Yara da dama sun mutu a gida kafin a kai su asibiti, wannan cuta ce mai saurin kisa.”

‘’Muna kira ga gwamnati da ta gaggauta daukar matakin ceto rayukan jama’a, daga wannan cuta wadda mun lura ta na dauke da zazzabi, tari, kashe jiki da sauransu.”

A nashi bangaren, jami’in kula da riga-kafi na karamar Hukumar Potiskum, Mallam Buba, ya musanta alkaluman wadanda suka mutu ta sanadin cutar, amma ya ce a kalla yara 42 ne ke kwance a asibiti.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

sallah
Manyan Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ya Ƙara Raguwa Zuwa Kashi 18.02%

October 15, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa

October 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Hana Manoma Girbi A Zamfara, Al’umma Na Neman Taimako

October 15, 2025
Next Post
Xi Ya Jaddada Bukatar Samar Da Sabon Tsarin Tattalin Arziki Mai Kara Bude Kofa 

Xi Ya Jaddada Bukatar Samar Da Sabon Tsarin Tattalin Arziki Mai Kara Bude Kofa 

LABARAI MASU NASABA

Sashen Cinikayyar Kamfanonin Sarrafa Hajoji Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso 4.7 Bisa Dari Cikin Watanni Tara Na Farkon Shekarar Nan

Sashen Cinikayyar Kamfanonin Sarrafa Hajoji Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso 4.7 Bisa Dari Cikin Watanni Tara Na Farkon Shekarar Nan

October 15, 2025
Kafafen Sada Zumunta Na Zamani Suna Taimakawa Wajen Ta’azzara Matsalar Tsaro A Arewa – Yari 

Kafafen Sada Zumunta Na Zamani Suna Taimakawa Wajen Ta’azzara Matsalar Tsaro A Arewa – Yari 

October 15, 2025
Nazarin CGTN: Jamaar Duniya Sun Yi Ammana Amurka Za Ta Fi Jin Jiki Daga Yakin Haraji 

Nazarin CGTN: Jamaar Duniya Sun Yi Ammana Amurka Za Ta Fi Jin Jiki Daga Yakin Haraji 

October 15, 2025
Kotu Ta Ɗaure Mai Horas Da ‘Yan Wasa Shekaru 8 Sakamakon Zargin Luwaɗi Da Ƙaramin Yaro A Kano

Kotu Ta Ɗaure Mai Horas Da ‘Yan Wasa Shekaru 8 Sakamakon Zargin Luwaɗi Da Ƙaramin Yaro A Kano

October 15, 2025
Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Ƙasar Madagascar

Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Ƙasar Madagascar

October 15, 2025
Shugaban Zaunannen Kwamitin Majalisar Wakilan Jama’ar Sin Ya Gana Da Mukaddashin Shugaban Majalisar Dattawan Kasar Liberia

Shugaban Zaunannen Kwamitin Majalisar Wakilan Jama’ar Sin Ya Gana Da Mukaddashin Shugaban Majalisar Dattawan Kasar Liberia

October 15, 2025
Gwamnan Kaduna Ya Taya Al’Amin Murnar Nasarar Lashe Gasar Ƙirƙirar Fasaha Ta Duniya A Ƙasar Birtaniya 

Gwamnan Kaduna Ya Taya Al’Amin Murnar Nasarar Lashe Gasar Ƙirƙirar Fasaha Ta Duniya A Ƙasar Birtaniya 

October 15, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Ladan Bosso Ya Ajiye Aikin Horar Da Barau Fc 

Da Ɗumi-ɗumi: Ladan Bosso Ya Ajiye Aikin Horar Da Barau Fc 

October 15, 2025
An Bude Bikin Baje Kolin Kasuwanci Na Kasa Da Kasa Na 138 A Guangzhou

An Bude Bikin Baje Kolin Kasuwanci Na Kasa Da Kasa Na 138 A Guangzhou

October 15, 2025
sallah

Da Ɗumi-ɗumi: Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ya Ƙara Raguwa Zuwa Kashi 18.02%

October 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.