ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yanzu-yanzu: Hon. Buba Mashio Ya Zama Sabon Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Yobe

by Muhammad Maitela
3 years ago
Buba Mashio

Hon. Chiroma Buba Mashio daga mazabar Jajere, ya zama sabon Kakakin majalisar dokokin jihar Yobe, karo na 8.

 

Hakan ya biyo bayan zaman da majalisar ta kaddamar yau a zauren majalisar dake Damaturu, yayin da aka fara gabatar da kudirin zaben sabon Kakakin Majalisar, wanda Hon. Adamu Dala Dogo mai wakiltar mazabar Karasuwa ya gabatar inda ya samu goyon bayan Hon. Bukar Mustapha na mazabar Geidam ta tsakiya tare da samun amincewar dukkanin yan majalisar dokokin 24.

ADVERTISEMENT
  • Siyasa: Tsugune Ba Ta Kare Wa Tinubu Ba A Kotun Sauraren Kararrakin Zabe

An haifi Hon. Buba Mashio ranar 25 ga Mayu, a 1968 a garin Mashio a karamar hukumar Fune dake jihar Yobe.

 

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Ya fara karatun sa a firamaren Mashio sannan ya wuce Sakandaren Gwamnati dake Damagum, kuma ya fara aiki a karamar hukumar Fune inda ya yi murabus ya tsaya takarar kansila mai wakiltar gundumar Mashio, inda daga bisani ya zama mataimakin shugaban karamar hukumar.

 

A kokarinsa na cigaba da karatunsa, sabon Kakakin ya garzaya inda yayi Diploma a Ramat Polytechnic Maiduguri, da Digirinsa na farko a Jami’ar Maiduguri a fannin kimiyyar siyasa.

 

Mashio ya tsaya takarar dan majalisar dokokin jihar Yobe mai wakiltar mazabar Jajere a 1999, ya yi aiki a kwamitoci da mukamai daban-daban a zauren majalisar.

 

Sauran manyan kusoshin majalisar sun hada da mataimakin Kakakin majalisar, Hon. Yau Usman Dachia, Shugaban Majalisar, Hon. Nasiru Hassan Yusuf, Mataimakinsa, Hon. Hassan Muhd ​​Yusufari, Mai.Tsawatarwa a zauren majalisar, Hon. Muhammed Auwal Isa Bello, mataimakinsa, Hon. Ahmed Musa Dumbu.

 

A jawabinsa na godiya, sabon Kakakin majalisar, Chiroma Buba Mashio ya bayyana jin dadinsa ga takwarorinsa bisa ga damar da suka bashi ya jagoranci zauren majalisar na 8, tare da daukacin al’ummar jihar baki daya.

 

Mashio ya yi alkawarin samar da ingantaccen shugabanci “ba tare da nuna son kai ba; tsarin mulkin Tarayyar Nijeriya zai jagorance ni. Zan aiwatar da manufar bude kofa don maraba da shawarwari don inganta shugabanci nagari don samar da ingantacciyar doka.

 

Shugaban majalisar ya bada tabbacin yin aiki cikin kwanciyar hankali da bangaren zartaswa da bangaren shari’a domin a samar da shugabanci nagari a jihar Yobe.

Buba Mashio
Muhammad Maitela
+ postsBio
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    29 Ga Mayu: Gwamna Buni Zai Yi Tattaunawar Kai Tsaye Ta Farko Da Al’umma
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Wakilin VOA Haruna Dauda Ya Rasu A Maiduguri
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

MASU ALAKA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya
Labarai

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Next Post
Gwamnatin Kano Za Ta Sake Gina Shatale-talen Gidan Gwamnati Da Aka Rusa A Wajen Birnin Jihar

Gwamnatin Kano Za Ta Sake Gina Shatale-talen Gidan Gwamnati Da Aka Rusa A Wajen Birnin Jihar

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.