ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yanzu-yanzu: Hon. Buba Mashio Ya Zama Sabon Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Yobe

by Muhammad Maitela
3 years ago
Buba Mashio

Hon. Chiroma Buba Mashio daga mazabar Jajere, ya zama sabon Kakakin majalisar dokokin jihar Yobe, karo na 8.

 

Hakan ya biyo bayan zaman da majalisar ta kaddamar yau a zauren majalisar dake Damaturu, yayin da aka fara gabatar da kudirin zaben sabon Kakakin Majalisar, wanda Hon. Adamu Dala Dogo mai wakiltar mazabar Karasuwa ya gabatar inda ya samu goyon bayan Hon. Bukar Mustapha na mazabar Geidam ta tsakiya tare da samun amincewar dukkanin yan majalisar dokokin 24.

ADVERTISEMENT
  • Siyasa: Tsugune Ba Ta Kare Wa Tinubu Ba A Kotun Sauraren Kararrakin Zabe

An haifi Hon. Buba Mashio ranar 25 ga Mayu, a 1968 a garin Mashio a karamar hukumar Fune dake jihar Yobe.

 

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ya fara karatun sa a firamaren Mashio sannan ya wuce Sakandaren Gwamnati dake Damagum, kuma ya fara aiki a karamar hukumar Fune inda ya yi murabus ya tsaya takarar kansila mai wakiltar gundumar Mashio, inda daga bisani ya zama mataimakin shugaban karamar hukumar.

 

A kokarinsa na cigaba da karatunsa, sabon Kakakin ya garzaya inda yayi Diploma a Ramat Polytechnic Maiduguri, da Digirinsa na farko a Jami’ar Maiduguri a fannin kimiyyar siyasa.

 

Mashio ya tsaya takarar dan majalisar dokokin jihar Yobe mai wakiltar mazabar Jajere a 1999, ya yi aiki a kwamitoci da mukamai daban-daban a zauren majalisar.

 

Sauran manyan kusoshin majalisar sun hada da mataimakin Kakakin majalisar, Hon. Yau Usman Dachia, Shugaban Majalisar, Hon. Nasiru Hassan Yusuf, Mataimakinsa, Hon. Hassan Muhd ​​Yusufari, Mai.Tsawatarwa a zauren majalisar, Hon. Muhammed Auwal Isa Bello, mataimakinsa, Hon. Ahmed Musa Dumbu.

 

A jawabinsa na godiya, sabon Kakakin majalisar, Chiroma Buba Mashio ya bayyana jin dadinsa ga takwarorinsa bisa ga damar da suka bashi ya jagoranci zauren majalisar na 8, tare da daukacin al’ummar jihar baki daya.

 

Mashio ya yi alkawarin samar da ingantaccen shugabanci “ba tare da nuna son kai ba; tsarin mulkin Tarayyar Nijeriya zai jagorance ni. Zan aiwatar da manufar bude kofa don maraba da shawarwari don inganta shugabanci nagari don samar da ingantacciyar doka.

 

Shugaban majalisar ya bada tabbacin yin aiki cikin kwanciyar hankali da bangaren zartaswa da bangaren shari’a domin a samar da shugabanci nagari a jihar Yobe.

Buba Mashio
Muhammad Maitela
+ postsBio
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    29 Ga Mayu: Gwamna Buni Zai Yi Tattaunawar Kai Tsaye Ta Farko Da Al’umma
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Wakilin VOA Haruna Dauda Ya Rasu A Maiduguri
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
Gwamnatin Kano Za Ta Sake Gina Shatale-talen Gidan Gwamnati Da Aka Rusa A Wajen Birnin Jihar

Gwamnatin Kano Za Ta Sake Gina Shatale-talen Gidan Gwamnati Da Aka Rusa A Wajen Birnin Jihar

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.