• English
  • Business News
Thursday, August 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Rukunin Kamfanonin Dangote, Aliko Dangote ya zama attajirin da ya fi kowa kudi a Afirka karo na 12 a jere, kamar yadda mujallar Forbes ta ruwaito.

Babban kamfanin Dangote na siminti ne ya ci gaba kasancewa kan gaba wajen samar da siminti a Afirka, kuma Dangote shi ne dan Nijeriya daya tilo a cikin jerin attajirai 200 na farko a duniya wanda darajarsa tai kai dalar Amurka biliyan 14.2, sama da dala biliyan 12.1 da ya samu a bara.

  • Gwamnatin Kano Za Ta Dauki Nauyin Karatun Dalibai 1,100
  • Tinubu Ya Bada Umarnin Binciko Wadanda Suke Kashe-Kashe A Filato

A halin yanzu Dangote yana matsayi na 124 a cikin manyan attajiran duniya, kuma shi ne dan Nijeriya daya tilo a cikin jerin manyan attajiran duniya 200 kuma daya daga cikin ‘yan Afirka biyu da ke jerin attajirai; tare da Johann Rupert na Afirka ta Kudu, wanda ya zo na 157 da darajar dukiyar da ta kai dala biliyan 11.1.

Attajirin wanda ya fi kowa kudi a Afirka na jagorantar kamfanin siminti mafi girma a nahiyar Afrika.

Kamfanin siminti na Dangote na samar da tan miliyan 51.6 a kowace shekara a kasashe goma a Afrika, tare da hadakar masana’antu a kasashe bakwai da kuma wasu masana’antu a Kamaru da Ghana da Saliyo.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya

Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno

Dangote ya mallaki kamfanonin gishiri da sukari da ma wasu daban.

Kazalika, attajirin ya mallaki matatar tace mai, wadda ake kyautata zaton za ta zama mafi girma a duniya, wadda tsohon shugaban kasar Nijeriya, shugaba Buhari ya kaddamar kuma ana sa ran za ta sarrafa gangar mai 650,000 don amfanin cikin gida da kuma fitar da shi zuwa kasashen waje.

Mujallar Fortune, wata mujalla ce ta kasuwanci ta kasa da kasa da ke Amurka, ta ayyana Dangote a matsayi na 11 cikin mutum 50 mafi tasiri a duniya a tsakanin ‘yan kasuwa maza da mata.

Mujallar da aka fara buga ta a watan Fabrairun 1930, ta ce attajirim na sauya duniya tare da zaburar da wasu a harkokin kasuwanci da gwamnati wajen ciyar da al’ummarsu gaba.

Dangote ya samu matakin ne bayan da mujallar ta ce attajirin yana amfani da dukiyarsa ta hanyar taimakon jama’a ta gidauniyarsa ta Aliko Dangote.

Mutum 10 maza da mata da mujallar Fortune ta zayyano a matsayin wadanda suka fi kowa tasiri su ne: Bill da Melinda Gates, Jacinda Ardem, Robert Mueller, Pony Ma, Satya Nadella, Greta Thunberg, Margrethe Vestager, Anna Nimiriano, Jose Andres, da Dough Mcmillon da Lisa Woods.

Shi kuwa Dangote an ayyana shi a matsayin daya daga cikin manyan ‘yan kasuwa a fadin duniya wanda ya cancanci a karrama shi ta hanyar basirar kasuwancinsa da kuma ayyukan alheri.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArzikiAttajiriDangoteMujallar ForbesMujallar FortuneSiminti
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hatsarin Mota Ya Yi Ajalin Mutum 5 A Enugu

Next Post

Mark Zuckerberg Ya Fara Daukar Horo Don Yin Dambe Da Elon Musk

Related

Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya
Manyan Labarai

Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya

8 hours ago
Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno

14 hours ago
Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82
Manyan Labarai

Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82

15 hours ago
Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano
Da É—umi-É—uminsa

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

1 day ago
Remi Tinubu Ta Bada Gudunmawar Naira Biliyan 1 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwan Neja Ta Shafa
Manyan Labarai

Remi Tinubu Ta Bada Gudunmawar Naira Biliyan 1 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwan Neja Ta Shafa

1 day ago
Shugaban ‘Yan Bindiga A Zamfara, Bello Turji, Ya Ajiye Makamai, Ya Saki Mutane 32
Manyan Labarai

Shugaban ‘Yan Bindiga A Zamfara, Bello Turji, Ya Ajiye Makamai, Ya Saki Mutane 32

1 day ago
Next Post
Mark Zuckerberg Ya Fara Daukar Horo Don Yin Dambe Da Elon Musk

Mark Zuckerberg Ya Fara Daukar Horo Don Yin Dambe Da Elon Musk

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

August 6, 2025
Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

August 6, 2025
Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

August 6, 2025
Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

August 6, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Bayar Da Kiwon Lafiya Kyauta Ga ‘Yan Fansho Masu Karamin Karfi 

August 6, 2025
Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

August 6, 2025
Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano

Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano

August 6, 2025
Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

August 6, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake ÆŠage Ranar Komawa Makarantu

“Ku Yi Murabus Idan Baza Ku Iya Rike Amanar Jama’a ba” – Gargadin Gwamna Abba Ga Kwamishinoninsa

August 6, 2025
Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza

Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza

August 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.