• English
  • Business News
Wednesday, October 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

by Sadiq
2 years ago
Dangote

Shugaban Rukunin Kamfanonin Dangote, Aliko Dangote ya zama attajirin da ya fi kowa kudi a Afirka karo na 12 a jere, kamar yadda mujallar Forbes ta ruwaito.

Babban kamfanin Dangote na siminti ne ya ci gaba kasancewa kan gaba wajen samar da siminti a Afirka, kuma Dangote shi ne dan Nijeriya daya tilo a cikin jerin attajirai 200 na farko a duniya wanda darajarsa tai kai dalar Amurka biliyan 14.2, sama da dala biliyan 12.1 da ya samu a bara.

  • Gwamnatin Kano Za Ta Dauki Nauyin Karatun Dalibai 1,100
  • Tinubu Ya Bada Umarnin Binciko Wadanda Suke Kashe-Kashe A Filato

A halin yanzu Dangote yana matsayi na 124 a cikin manyan attajiran duniya, kuma shi ne dan Nijeriya daya tilo a cikin jerin manyan attajiran duniya 200 kuma daya daga cikin ‘yan Afirka biyu da ke jerin attajirai; tare da Johann Rupert na Afirka ta Kudu, wanda ya zo na 157 da darajar dukiyar da ta kai dala biliyan 11.1.

Attajirin wanda ya fi kowa kudi a Afirka na jagorantar kamfanin siminti mafi girma a nahiyar Afrika.

Kamfanin siminti na Dangote na samar da tan miliyan 51.6 a kowace shekara a kasashe goma a Afrika, tare da hadakar masana’antu a kasashe bakwai da kuma wasu masana’antu a Kamaru da Ghana da Saliyo.

LABARAI MASU NASABA

Da Ɗumi-ɗumi: Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ya Ƙara Raguwa Zuwa Kashi 18.02%

2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa

Dangote ya mallaki kamfanonin gishiri da sukari da ma wasu daban.

Kazalika, attajirin ya mallaki matatar tace mai, wadda ake kyautata zaton za ta zama mafi girma a duniya, wadda tsohon shugaban kasar Nijeriya, shugaba Buhari ya kaddamar kuma ana sa ran za ta sarrafa gangar mai 650,000 don amfanin cikin gida da kuma fitar da shi zuwa kasashen waje.

Mujallar Fortune, wata mujalla ce ta kasuwanci ta kasa da kasa da ke Amurka, ta ayyana Dangote a matsayi na 11 cikin mutum 50 mafi tasiri a duniya a tsakanin ‘yan kasuwa maza da mata.

Mujallar da aka fara buga ta a watan Fabrairun 1930, ta ce attajirim na sauya duniya tare da zaburar da wasu a harkokin kasuwanci da gwamnati wajen ciyar da al’ummarsu gaba.

Dangote ya samu matakin ne bayan da mujallar ta ce attajirin yana amfani da dukiyarsa ta hanyar taimakon jama’a ta gidauniyarsa ta Aliko Dangote.

Mutum 10 maza da mata da mujallar Fortune ta zayyano a matsayin wadanda suka fi kowa tasiri su ne: Bill da Melinda Gates, Jacinda Ardem, Robert Mueller, Pony Ma, Satya Nadella, Greta Thunberg, Margrethe Vestager, Anna Nimiriano, Jose Andres, da Dough Mcmillon da Lisa Woods.

Shi kuwa Dangote an ayyana shi a matsayin daya daga cikin manyan ‘yan kasuwa a fadin duniya wanda ya cancanci a karrama shi ta hanyar basirar kasuwancinsa da kuma ayyukan alheri.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

sallah
Manyan Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ya Ƙara Raguwa Zuwa Kashi 18.02%

October 15, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa

October 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Hana Manoma Girbi A Zamfara, Al’umma Na Neman Taimako

October 15, 2025
Next Post
Mark Zuckerberg Ya Fara Daukar Horo Don Yin Dambe Da Elon Musk

Mark Zuckerberg Ya Fara Daukar Horo Don Yin Dambe Da Elon Musk

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Kaduna Ya Taya Al’Amin Murnar Nasarar Lashe Gasar Ƙirƙirar Fasaha Ta Duniya A Ƙasar Birtaniya 

Gwamnan Kaduna Ya Taya Al’Amin Murnar Nasarar Lashe Gasar Ƙirƙirar Fasaha Ta Duniya A Ƙasar Birtaniya 

October 15, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Ladan Bosso Ya Ajiye Aikin Horar Da Barau Fc 

Da Ɗumi-ɗumi: Ladan Bosso Ya Ajiye Aikin Horar Da Barau Fc 

October 15, 2025
An Bude Bikin Baje Kolin Kasuwanci Na Kasa Da Kasa Na 138 A Guangzhou

An Bude Bikin Baje Kolin Kasuwanci Na Kasa Da Kasa Na 138 A Guangzhou

October 15, 2025
sallah

Da Ɗumi-ɗumi: Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ya Ƙara Raguwa Zuwa Kashi 18.02%

October 15, 2025
Mujallar “Qiushi” Za Ta Wallafa Muhimmiyar Kasidar Shugaba Xi Jinping Kan Muhimman Shawarwari Hudu Da Ya Gabatar

Mujallar “Qiushi” Za Ta Wallafa Muhimmiyar Kasidar Shugaba Xi Jinping Kan Muhimman Shawarwari Hudu Da Ya Gabatar

October 15, 2025
Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Dajin Taraba

Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Dajin Taraba

October 15, 2025
Xi Jinping Ya Taya Patrick Herminie Murnar Lashe Zaben Shugaban Kasar Seychelles

Xi Jinping Ya Taya Patrick Herminie Murnar Lashe Zaben Shugaban Kasar Seychelles

October 15, 2025
Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu

Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu

October 15, 2025
Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

October 15, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa

October 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.