• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Neja Ta Umarci Masu Gidaje A Hanyoyin Ruwa Su Tashi

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Neja Ta Umarci Masu Gidaje A Hanyoyin Ruwa Su Tashi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Neja ta bukaci mazauna yankunan da suka gina gidaje a kan magudanan ruwa da su yi gaggawar tashi don kaucewa ambaliyar ruwa.

Mataimakin gwamnan jihar, Yakubu Garba ne, ya ba da umarnin a ranar Laraba, yayin ziyarar duba wasu yankuna da ambaliyar ruwa ta shafa, biyo bayan mamakon ruwan sama da aka yi a daren ranar Talata a Minna, babban birnin jihar.

  • ‘Yansanda Sun Cafke Wasu Mutum 5 Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Jihar Jigawa
  • Jakadan Sin A Nijeriya Ya Gana Da Shugaban APC Ta Kasar

Ya kuma umarci hukumar raya birane ta jihar da hukumar bada agajin gaggawa ta jihar (NSEMA) da hukumar kare muhalli ta jihar (NISEPA), da su wayar da kan jama’ar da ke zaune a magudanan ruwa domin su tashi.

“Ina jajanta wa wadanda da ambaliyar ruwan daren jiya ta shafa.

“Ya zama wajibi mu tabbatar da cewa an ceto rayuka da dukiyoyi.

Labarai Masu Nasaba

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

“Saboda haka, na ba hukumomin gwamnati da suka dace da su duba gidaje da gine-ginen da aka yi a kan hanyoyin ruwa sannan su tashi mazauna yankunan.

“Wannan wani mataki me kaucewa sake aukuwar ambaliyar ruwaa nan gaba,” a cewarsa.

Mataimakin gwamnan ya kuma shawarci jama’a da su guji sayen filaye a magudanan ruwa don kaucewa tafka asara.

Ya kuma gardadi jama’ar jihar da su daina zubar da shara a magudanan ruwa don hakan na haifar da ambaliyar ruwa.

Shugaban Hukumar Raya Birane, Alhaji Ahmad Bako, ya ce tuni aka sanya wa gine-ginen da ke kan magudanan ruwa jan fenti da nufin rushe su.

Bako ya kara da cewa tuni aka bai wa masu wurin wa’adin tashi tare da takardar izinin rushe gine-ginen.

Wasu daga cikin wuraren da za a tayar sun hada da titin Brighter Road, Sabuwar Kasuwa da ke yankin Maitumbi, Gurara da kuma Gbaganu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ambaliyar RuwagwamnatiNeja
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jakadan Sin A Nijeriya Ya Gana Da Shugaban APC Ta Kasar

Next Post

‘Yan Majalisar Dokokin Nijeriya Sun Bukaci Karin Albashi

Related

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark
Labarai

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

55 minutes ago
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara
Labarai

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

4 hours ago
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace
Labarai

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

5 hours ago
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

15 hours ago
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta
Labarai

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

17 hours ago
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson
Siyasa

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

19 hours ago
Next Post
‘Yan Majalisar Dokokin Nijeriya Sun Bukaci Karin Albashi

'Yan Majalisar Dokokin Nijeriya Sun Bukaci Karin Albashi

LABARAI MASU NASABA

Super Falcons Zasu Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Zasu Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

July 27, 2025
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

July 27, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.