ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Cafke Wasu Mutum 5 Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Jihar Jigawa

by Muhammad
3 years ago
'Yansanda

Rundunar ‘Yansandan jihar Jigawa ta ce ta kama wasu mutane biyar da ake zargin ‘yan fashi da makami ne a wana samame suka gudanar a jihar.

Wata sanarwa da kakakin rundunar ‘Yansandan jihar, Lawal Shiisu, ya fitar a ranar Laraba a Dutse, ya bayyana cewa an kama biyu daga cikin wadanda ake zargi da laifin fashin wani direban babur.

  • ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Yi Wa Jama’a Kutse A Asusun Banki
  • Jami’an Tsaro Sun Yi Kwanton Bauna Sun Kashe ‘Yan Fashin Daji 10 A Kaduna

Ya ce wanda abin ya ritsa da shi, Ashiru Musa, na kauyen Kyran, ya kai rahoton lamarin ga ofishin ‘yansanda na Fanisau.

ADVERTISEMENT

Marigayin ya bayyana cewa ‘yan bindigar biyu dauke da makamai ne suka tare shi inda suka tafi da babur dinsa mai lamba AYE 918 UP Ogun.

Shisu ya ce, ‘yan sintiri da ke aiki a yankin Fanisau sun yi kokarin bin sawun ‘yan fashi da makamin inda suka samu nasarar kwato babur din.

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Da ‘Yan Sa-kai Sun Ceto Shanu 245 Da Aka Sace A Kaduna

An Daure Mutum Biyu Shekara 24 Saboda Kashe Wani Dan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

Kakakin rundunar ‘yan sandan ya bayyana sunayensu ‘yan Fashin da suka hada da Tijjani Haruna mai shekaru 19 da kuma Baballe Abdulrahman mai shekaru 25.

Kakakin ya ce jami’an ‘yan sanda da ‘yan banga na karamar hukumar Ringim sun kuma kama wasu mutum uku da ake zargi.

Wadanda ake zargin su ne, Ahmadu Audu da Shuaibu Bayeri da kuma Samaila Musa, wadanda suka fito daga kauyen Majiyar Kirdau a karamar hukumar Ringim, an kama su ne bisa laifin hada baki, fashi da makami da kuma haddasa munanan raunuka.

Shiisu ya ce, wadanda ake zargin sun amsa laifin sace babura da dama a karamar hukumar Ringim da kewaye.

Ya kara da cewa, “Sun kuma ambaci wasu gungun ‘yan bindiga da kuma wanda suke taimaka musu a karamar hukumar Gezawa ta jihar Kano.”

Shiisu ya ce za a gurfanar da wadanda ake zargin zuwa kotu bayan kammala bincike.

'Yansanda
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Da ‘Yan Sa-kai Sun Ceto Shanu 245 Da Aka Sace A Kaduna

June 6, 2026
Nijeriya Ta Yi Nasara A Kotun Ingila Kan Rikicinta Da Kamfanin P&ID
Kotu Da Ɗansanda

An Daure Mutum Biyu Shekara 24 Saboda Kashe Wani Dan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

June 6, 2026
NSCDC Ta Sallami Ma’aikatan Sa-kai Biyar A Kano Saboda Rashin Da’a
Kotu Da Ɗansanda

NSCDC Ta Sallami Ma’aikatan Sa-kai Biyar A Kano Saboda Rashin Da’a

June 6, 2026
Next Post
Jakadan Sin A Nijeriya Ya Gana Da Shugaban APC Ta Kasar

Jakadan Sin A Nijeriya Ya Gana Da Shugaban APC Ta Kasar

LABARAI MASU NASABA

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

June 13, 2026
Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

June 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.