• English
  • Business News
Sunday, May 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Mai Fada Da Cikawa

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasar Sin Mai Fada Da Cikawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A karo na uku a dan tsakanin nan, wani babban jami’in Amurka na ziyara a kasar Sin. Sai dai a wannan karo, mai ziyarar shi ne jakadan Amurka mai kula da batun sauyin yanayi wato John Kerry. Ana sa ran yayin ziyararsa daga ranar 16 zuwa 19 ga wata, zai tattauna da bangaren kasar Sin kan batun sauyin yanayi, musamman game da yadda za a rage fitar da hayakin carbon a matsayinsu na kasashen da suka fi fitar da hayaki a duniya.

A ganina, ziyarar ta John Kerry ta zo a kan gaba, kuma a inda ya dace, la’akari da namijin kokarin da kasar Sin ke ci gaba da yi da zummar shawo kan matsalar.

  • Firaministan Sin Ya Gana Da Wakilin Amurka Kan Sauyin Yanayi

Wani abu da na fahimta dangane da kasar Sin shi ne, ba ta daukar alkawarin fatar baki, ita mai fada da cikawa ce. Ina sa ran kasar Sin za ta cimma burinta na kaiwa matsayin koli wajen fitar da hayakin carbon a shekarar 2030, tare da a samun daidaito tsakanin yawan hayakin da za ta fitar da abubuwan da za su shawo kansa ya zuwa 2060. Tabbas tuni kasar Sin ta dau hanya domin ta dade da fara aiwatar da abubuwa, kamar dashen bishiyoyi da dazuzukan da kyautata jituwa tsakanin dan adam da muhallinsa da sarrafa shawa da amfani da kyautata amfani da makamashi mai tsafta da sauransu. Ina da yakinin Sin za ta cimma burinta kafin lokacin da ta ayyana.

Kuma na lura cikin dukkan wasu ayyukan kasar, ta kan mayar da hankali ne wajen ganin ta rage fitar da hayakin da ma duk wani abu da ka iya gurbata muhalli. Wannan ya tuna min da ziyarata ta baya-bayan nan a birnin Chengdu na lardin Sichuan, wato birnin da zai karbi bakuncin gasar wasannin daliban jami’o’i ta duniya, inda na ga yadda kasar ta shirya tsaf domin takaita abubuwan da ka iya gurbata muhalli. Misali, yadda motocin sufurin yayin gasar ke amfani da makamashi mai tsafta da yadda aka samar da na’urorin samar da lantarki daga makamashi mai tsafta da sauransu.

Haka zalika, su ma jama’ar kasar Sin suna kokarin rungumar hanyar da ta dace na rage fitar da hayaki mai guba. Misali, bayanai sun nuna cewa, a rabin farkon bana kadai, an yi wa kimanin sabbin motoci miliyan 3.13 masu amfani da sabon makamashi rejista, adadin da ya karu da kaso 41.6 a kan na bara, wanda kuma ya kai matsayin koli.

Labarai Masu Nasaba

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

Dama dai Amurka ce ke jan kafa kan batun sauyin yanayi inda take kokarin mayar da hannu agogo baya game da yarjejeniyoyin da aka cimma da kuma kin cika alkawurranta. Fatan ita ce yadda manyan jami’anta ke zarya a kasar Sin, ya kasance ta cika alkawuranta ta kuma dauki darasi daga kasar Sin, tare da hada hannu da ita wajen tabbatar da kafuwar duniya mai aminci da tsaro makoma ta bai daya ga daukacin bil adama.

 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Uba Sani Ya Rantsar Da Manyan Jami’an Gwamnati Biyu A Jihar Kaduna

Next Post

Gwamnan Zamfara Ya Kai Wa Mangal Ziyarar Ta’aziyya

Related

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara
Daga Birnin Sin

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

12 hours ago
An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva
Daga Birnin Sin

An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

13 hours ago
Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu
Daga Birnin Sin

Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

15 hours ago
Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali
Daga Birnin Sin

Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

18 hours ago
Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Daban-Daban A Moscow
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Daban-Daban A Moscow

18 hours ago
Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo
Daga Birnin Sin

Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

1 day ago
Next Post
Gwamnan Zamfara Ya Kai Wa Mangal Ziyarar Ta’aziyya

Gwamnan Zamfara Ya Kai Wa Mangal Ziyarar Ta'aziyya

LABARAI MASU NASABA

Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

May 11, 2025
Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

May 11, 2025
Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

May 11, 2025
Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

May 11, 2025
Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

May 10, 2025
An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

May 10, 2025
Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

May 10, 2025

Kungiyar Malaman Jami’o’i Ta Ba Dalibai 164 Tallafin Karatu

May 10, 2025
Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)

Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)

May 10, 2025
Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

May 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.